Dahiru Mangal

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Dahiru Mangal
Rayuwa
Haihuwa Katsina, 1957 (66/67 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan kasuwa

Dahiru Barau Mangal (an haife shi ne a ranar 3 ga watan Agustan, shekara ta alif ɗari tara da hamsin da bakwai 1957A.c) ɗan kasuwa ne a Najeriya. Shi ne ya kafa kamfanin jiragen sama na Max Air a shekara ta 2008.[1]

Rayuwar farko[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Dahiru Barau Mangal a cikin jihar Katsina ga dangin Alhaji Barau Mangal. Ya girma tare da 'yan'uwansa Alhaji Bashir Barau Mangal, Alhaji Hamza Barau Mangal, Hajiya Zulai Barau Mangal, Hajiya Yar Goje da Mahaifiyarsa Hajiya Murjanatu Barau Mangal a Katsina. Ya fara kasuwancinsa a matsayin direban babbar mota kuma daga baya ya cigaba da sayen motoci domin haya.

Ayyuka[gyara sashe | gyara masomin]

Mangal shi ne wanda ya kafa kamfanin jiragen sama na Max Air, wanda yake jagorantar kamfanin jirgin sama na cikin gida, yanki da kuma na kasashen duniya. Sauran bangarorin da ya sa hannun jari sun hada da sufuri, mai da gas da kuma gini. Ya kasance Babban Daraktan Kamfanin MRS Oil Nigeria Plc wanda ya yi murabus a ranar 17 ga watan Nuwamban, shekara ta 2017.[2]

Shi babban mai hannun jari ne a kamfanin na Oando Plc inda ya samu sabani da shugabannin kamfanin wanda ya kai ga dakatar da kasuwancin Oando a kasuwar kasuwannin hada-hadar hannayen jari ta Legas da ta Johannesburg. Rikicin ya samo asali ne a shekara ta 2017 lokacin da Mangal tare da wani kamfanin mai suna Gabriel Volpi da ke sarrafa harsashi suka rubuta takardar koke ga hukumar musayar hannayen jari ta Najeriya kan zargin almubazzaranci da kudi da shugabannin Oando suka yi, wanda hakan ya sa hukumar ta binciki lamarin har da yiwuwar cinikin mai ciki. An warware rikicin ne ta hanyar sa hannun Mai Martaba Sarkin Kano, Sanusi Lamido Sanusi a watan Janairun Shekara ta 2018.

Kyauta[gyara sashe | gyara masomin]

Mangal sanannen ɗan agaji ne wanda ke ba da taimako da tallafi ga ɗalibai, mutanen da ke da nakasa da kuma ’yan gudun hijirar da ke cikin gida da rikici ya shafa a Nijeriya. Haka nan yana raba abinci a yankin Arewacin Najeriya da suka hada da Katsina, Kano, Kaduna da kauyuka a kowace rana.Dahiru ya kasance daya daga cikin masu arzikin da ke kiyayewa wurin bayar da zakka a lokacin Satan ramadana

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

 

  1. Www.bbc hausa. com
  2. Www.Max air. Com