Sanusi Lamido Sanusi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

â

Sanusi Lamido Sanusi
Masarautar Kano

8 ga Yuni, 2014 -
Ado Bayero
Governor of the Central Bank of Nigeria (en) Fassara

3 ga Yuni, 2009 - 20 ga Faburairu, 2014
Rayuwa
Haihuwa Kano, 31 ga Yuli, 1961 (62 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
King's College, Lagos (en) Fassara
Sana'a
Sana'a Ma'aikacin banki da Malami
Imani
Addini Musulunci

Sanusi Lamido SanusiAbout this soundSanusi Lamido Sanusi  (An haife shi 31 ga watan Yuni, alif ɗari tara da sittin da ɗaya( 1961) miladiyya Isa dan Maryam. Ɗan gidan sarautar Kano ne kuma tsohon Shugaban babban bankin Nijeriya (CBN). A yanzun sarkin Kano na 14, an naɗa shi sarauta ne a ranar takwas ga watan Yuni na shekara ta dubu biyu da goma sha huɗu, 2014 bayan rasuwar tsohon sarkin Kano Ado Bayero.[1] Zuwa 9 ga watan march shekara ta dubu biyu da ashirin, 2020. Sarki Sanusi ma'aikacin banki ne, wanda shine tsohon Shugaban Babban Bankin Nijeriya. Wanda ya riƙe muƙamin tun daga uku (3) ga watan Yuni na shekara ta dubu biyu da tara, 2009, da yayi tsawon shekara biyar akai, kamar yadda dokar mukamin ya tabbatar amma sai dai Sanusin bai cika shekarunsa ba inda tsohon shugaban ƙasa na waccan lokaci, wato Goodluck Jonathan ya tsige shi a ranar ashirin ga watan February shekara ta dubu biyu da goma sha huɗu, 2014, sanadiyar Sanusi ya bankaɗo wani zargi na badaƙalar kuɗi $20 billion a hukumar matatar man fetur na ƙasa (NNPC).

Sanusi a wurin taro akan tattalin arziki a 2013
Sarki Sanusi
Sanusi lamido

Sanusi jika ne na Sarkin Kano Muhammadu Sanusi I, Sarki na 11th cikin sarakunan Fulani Na Kano.[2] Ma'aikacin banki ne kuma babban mutum ne, Malamin addinin musulunci ne da ake girmamawa.[3] Tun bayan sauƙe sarkin Kano Sanusi na II da gwamnatin jahar ta yi daga sarautar Kano, inda ya koma jihar Legas da zama, tsohon sarkin ya kai ziyarar sa ta farko a jihar Kaduna a ranar 23 Augusta 2020. Inda yazo dan girmama aikin da gwamnan jihar Malam Nasiru El-Rufai ya bashi tun bayan sauke shi daga kujerarsa [4]

Sarki Sanusi

.

Tsige shi[gyara sashe | gyara masomin]

Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje ranar 9 ga watan maris shekara ta dubu biyu da ashirin, 2020 ya sauke shi daga kan karagar mulki.[5] [6]

Gwamnatin ta bayyana wasu dalilai dayasa suka sauke shi daga kan mulki, dalilan sun hada da:[7]

  • Rashin Biyayya;

Rashin halartar tarukan da gwamnati ke gayyatarsa ba tare da bada kwakkwaran dalili ba “Hakan rashin biyayyane,” inji sanarwar gwamnatin.

  • Kare mutuncin Kano;

Kare Mutunci, al`ada da addini gami da kimar masarautar mai dadadden tarihi wacce aka kafa ta shekaru dubbai da suka shude na daga cikin dalilan da suka sa aka dau matakin sauke sarkin. Inji sanarwar.

  • Sukar manufofin gwamnati;

Sarkin ya soki shirin gwamnatin jahar na ciwo bashi daga kasar chaina domin aiwatar da gina layin dogo a cikin birnin na kano yasa wasu da dama ke ganin na daga cikin dalilan da yasa aka sauke tsohon sarkin.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. http://www.nigerianbiography.com/2015/10/biography-of-sanusi-lamido-sanusi.html
  2. "Mr. Sanusi Lamido Aminu Sanusi". Central Bank of Nigeria.
  3. "The Role of Islam in Nigeria". The University of Georgia.
  4. https://news-af.feednews.com/news/detail/e000c9371ed4f08ef484ce3461ad6a64?client=news
  5. https://dailypost.ng/2020/03/09/breaking-emir-of-kano-muhammadu-sanusi-dethroned/
  6. https://www.bbc.com/news/world-africa-51804764
  7. https://www.bbc.com/hausa/labarai-51803542

. . . . . . .