Fasa gidan yari a Ekiti

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Fasa gidan yari a Ekiti
prison escape (en) Fassara
Bayanai
Kwanan wata 30 Nuwamba, 2014
Wuri
Map
 7°40′N 5°15′E / 7.67°N 5.25°E / 7.67; 5.25

Fasa gidan yarin na Ekiti wani hari ne da wasu ‘yan bindiga su 60 da ba a san ko su wanene ba suka kai a gidan yarin gwamnatin tarayya dake Afao road, Ado Ekiti a birnin jihar Ekiti dake kudu maso yammacin Najeriya.[1] Harin ya faru ne a ranar 30 ga watan Nuwamba, 2014,[2]fursunoni 341 sun tsere daga gidan yarin inda suka kashe mai gadi 1 da karnuka 20 na maharba.[3][4] Fursunonin da suka tsere dai suna jiran shari'a ne.[5] Fursunoni 10 da suka yi yunƙurin tserewa an kama su a yayin harin da aka yi ta musayar wuta tsakanin ƴan sanda da ‘yan bindigar.[6] An sake kama fursunoni 67 bayan harin, kuma fursunoni 274 sun tsere.[7] Wani fursuna wanda ya yi ikirarin cewa ya gudu ne a lokacin da ya ji karar harbe-harbe, ya koma gidan yarin ne domin ya cika takaitaccen hukuncin da aka yanke masa.[8]

Lamarin[gyara sashe | gyara masomin]

An ruwaito lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, 30 ga Nuwamba, 2014.[9] Kehinde Fadipe, Kwanturolan Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Najeriya, ya ƙaryata iƙirarin cewa ƴan bindigar da ba a san ko su wanene ba ƴan ƙungiyar Boko Haram ne,[10] wata ƙungiyar ta'adanci a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya, ta ce babu ɗaya daga cikin mambobinsu da ke jiran shari’a, a cikin wannan kurkukun.[11][12][13]

Zargi[gyara sashe | gyara masomin]

A ranar 1 ga Disamba, 2014, gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya zargi jami’an gidan yarin da haɗa baki da wasu ƴan bindiga da ba a san ko su wanene ba wajen kai harin.[14]

Martani[gyara sashe | gyara masomin]

Da farko dai harin na da alaƙa da ƙungiyar Oduduwa People’s Congress, wadda ake zargin yunkurin ne na sakin Adeniyi Adedipe, ba bisa ka'ida ba. Ya kasance Kodinetan na ƙungiyar Oodua Peoples Congress reshen jihar Ekiti, wanda ya daɗe yana jiran shari’a.[15][16] An samu Adedipe ne da laifin kisan tsohon shugaban ƙungiyar ma’aikatan tituna ta kasa, Cif Omolafe Aderiye.[17] Wannan ya haifar da martani da cece-kuce da dama a faɗin jihar, musamman tsakanin jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP[18] da jam’iyyar adawa, All Progressive Congress, APC,[19] amma aka soke iƙirarin cewa OPC ce ta kai harin. saboda Fadipe bai taɓa tserewa ba kamar yadda aka yi zargin a baya.[20][21][22]

Fasa gidan yarin dai ya biyo bayan rashin isassun ma’aikatan gidan yari da kayan aikin da gwamnatin tarayya ke samarwa wa gidajen yari.[23]

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "EKITI JAILBREAK: FG sets up probe panel". Vanguard News. 2 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  2. Sam Nwaoko - Ado-Ekiti. "Mayhem as gunmen invade Ekiti prison, free inmates". Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  3. "Gunmen invade Ekiti prison, kill warder, 20 dogs". thenigerianvoice.com. Retrieved 24 December 2014.
  4. Yinka Olugbade. "Jailbreak In Ekiti, Over 100 Inmates Escape, 1 Warder Killed". Nigerian Current. Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  5. "1 Killed As Suspected Boko Haram Members Attack Ekiti - Nigerian News from Leadership Newspapers". Nigerian News from Leadership Newspapers. Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  6. "Ekiti jailbreak: 67 prison inmates re-arrested". DailyPost Nigeria. 3 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  7. Akinlolu Oluwamuyiwa. "Guardian News Website - '274 inmates still missing after Ado-Ekiti jailbreak'". Archived from the original on 23 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  8. "Gunmen attack Ekiti prison, kill warder, 20 dogs". The Punch - Nigeria's Most Widely Read Newspaper. Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  9. "Kidnap, jailbreak: Nightmares in Ado-Ekiti « Nigeria pilot". Archived from the original on 23 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  10. Akinlolu Oluwamuyiwa. "Guardian News Website - Blast rocks Ado Ekiti prison". Archived from the original on 23 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  11. "Are Recent Prison Breaks in Nigeria Part of a Southward Expansion by Boko Haram?". IPI Global Observatory. 16 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  12. "Possible Boko Haram Gunmen Free More Than 200 Inmates In Nigeria Jailbreak". The Huffington Post. Archived from the original on 23 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  13. "More than 200 freed in Nigeria mass jailbreak". Retrieved 24 December 2014.
  14. "Governor Fayose Says Prison Officials Conspired With Inmates In Ekiti Prison Break". Channels Television. Retrieved 24 December 2014.
  15. "Prison Break In Ekiti As Gunmen Invade Ado Detention, All Prisoners 'Reportedly' Freed". NewsWireNGR. December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  16. "EKITI JAIL BREAK: APC accuses Fayose of complicity - Vanguard News". Vanguard News. 3 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  17. "APC Accuses Fayose Of Complicity In Ado Ekiti Jail Break - Nigerian News from Leadership Newspapers". Nigerian News from Leadership Newspapers. Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  18. "EKITI JAIL BREAK: APC accuses Fayose of complicity". Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  19. "Breaking News". Archived from the original on 2019-05-04. Retrieved 2023-01-22.
  20. "Ekiti prison attack an inside job – Fayose". The Punch - Nigeria's Most Widely Read Newspaper. Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  21. "Jailbreak: APC faults Fayose's aide on police report". Daily Independent, Nigerian Newspaper. Archived from the original on 24 December 2014. Retrieved 24 December 2014.
  22. "Metro - Ekiti Jailbreak: Escaped Prisoners Now Dining With Fayose in Govt. House?". Nigerian Bulletin - Trending News & Updates. Retrieved 24 December 2014.
  23. "Re-instate 'sacked' prisons officials". Vanguard News. 20 December 2014. Retrieved 24 December 2014.