Folashade Yemi-Esan
| Rayuwa | |
|---|---|
| Haihuwa | Jihar Kaduna, 13 ga Augusta, 1964 (61 shekaru) |
| ƙasa | Najeriya |
| Karatu | |
| Harsuna | Turanci |
| Sana'a | |
| Sana'a |
civil servant (en) |
Folashade Mejabi Yemi-Esan (née Mejabi; An haife ta a ranar 13 ga watan Agustan shekara ta 1964), ma'aikaciyar gwamnati ce ta ƙasar Najeriya kuma shugabar ma'aikatan gwamnati ta yanzu, tun daga ranar 4 ga watan Maris na shekara ta 2020. [1] Ta yi aiki a matsayin shugabar ma'aikatan gwamnati daga ranar 18 ga watan Satumbae shekarar 2019 har zuwa lokacin da ta rantsar da ita a ranar 4 ga Maris na shekarar 2020 biyo bayan dakatar da Winifred Ekanem Oyo-Ita.[2]
Rayuwa ta farko da ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Yemi-Esan a Jihar Kaduna, Najeriya . Ta fito ne daga Ikoyi, Ijumu, Jihar Kogi . Ta yi karatun firamare a Makarantar Bishop Smith, Ilorin sannan ta tafi Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Ilorin don karatun sakandare. Ta ci gaba zuwa Jami'ar Ibadan, inda ta kammala karatu a shekarar 1987 a matsayin mafi kyawun ɗaliban tiyata na haƙora. Daga baya ta sami takardar shaidar a cikin tsarin kiwon lafiya da gudanarwa, kafin ta sami digiri na biyu a cikin gwamnati da kuma gudanarwa ta duniya.[3]
Ayyuka
[gyara sashe | gyara masomin]Yemi-Esan ta fara aikinta a Ma'aikatar Lafiya ta Tarayya a ƙasar Najeriya, kafin ta ƙara Samun matsayi zuwa Darakta. A lokacin da take cikin ma'aikatar kiwon lafiya, ta yi aiki a matsayin jami'in hulɗa na Hukumar Lafiya ta Yammacin Afirka (WAHO), mai kula da lafiyar baki a cikin shirin makarantu da kuma darektan binciken tsara kiwon lafiya da ƙididdiga.[4][5]
A shekara ta 2012, an inganta ta zuwa matsayin Sakatare na Dindindin na Tarayya, tana aiki a matsayin Sakataren Dindindin Na Manufofin Sabis da Ofishin Dabarun Shugaban Ma'aikatan Jama'a na Tarayya. [6]
Shugaban ma'aikatan gwamnati
[gyara sashe | gyara masomin]A ranar 18 ga watan Satumbae shekarar 2019, shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ne ya naɗa ta a matsayin muƙaddashin shugaban ma'aikatan gwamnati na tarayyar, inda ta maye gurbin wanda aka dakatar da Winifred Ekanem Oyo-Ita . [7]
A ranar 28 ga watan Fabrairun Shekarar 2020, an sanya ta shugabar ma'aikatan gwamnati ta dindindin kuma an rantsar da ita a ofis a ranar 4 ga watan Maris na Shekarar 2020. [8][9] [10]
Kyaututtuka
[gyara sashe | gyara masomin]A watan Oktoba na shekara ta 2022, Shugaba Muhammadu Buhari ya ba ta lambar yabo ta ƙasa ta Najeriya ta Kwamandan Order of the Federal Republic (CFR). [11]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Jimoh, Abbas (28 February 2020). "Buhari retires Oyo-Ita, confirms Yemi-Esan as HoS". Daily Trust Newspaper. Archived from the original on 29 February 2020. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ "UPDATED: Buhari swears in Yemi-Esan as new HoS". The Punch Newspaper. 4 March 2020. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ "BUHARI APPOINT KOGI LADY ACTING HEAD OF SERVICE". Legacy Time. 19 September 2019. Retrieved 4 March 2020.[permanent dead link]
- ↑ Lawal, Nurudeen (19 September 2019). "Folasade Yemi-Esan: 7 things you should know about new head of service appointed by Buhari". Legit.ng. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ Awosiyan, Kunle. "Who Is Dr. Folashade Yemi-Esan, Acting HOS". Silverbird TV. Archived from the original on 9 October 2019. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ Royal, David (19 September 2019). "Six things you should know about the new Head of Service". Vanguard Newspaper. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ "Oyo-Ita out, Buhari appoints Folasade Yemi-Esan as acting HOS". P.M. News. 18 September 2019. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ Ogunyinka, Victor (29 February 2020). "Buhari finally 'retires' Oyo-Ita, names Esan substantive HoS". Vanguard Newspaper. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ Ogunmade, Omololu (4 March 2020). "Buhari Swears in Yemi-Esan as New Head of Service". This Day Newspaper. Retrieved 4 March 2020.
- ↑ https://www.vanguardngr.com/2015/10/buhari-appoints-oyo-ita-as-new-head-of-service/
- ↑ "FULL LIST: 2022 National Honours Award Recipients The Nation Newspaper" (in Turanci). 2022-10-09. Retrieved 2022-10-26.