Gani Odutokun

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Gani Odutokun
Rayuwa
Haihuwa Ghana, 9 ga Augusta, 1946
ƙasa Najeriya
Ghana
Mutuwa 16 ga Faburairu, 1995
Yanayin mutuwa  (traffic collision (en) Fassara)
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a painter (en) Fassara da Malami

Gani Odutokun (Agusta 9, 1946 - Fabrairu 15, 1995) ɗan Najeriya ne mai zane-zane ya shahara wajen ba da gudummawa da kuma renon mawaƙa a cikin al'ummar fasahar a garin Zariya dake a Nigeria. Ayyukansa sun haɗa da Allon bango, zane-zane da ƙirar murfin littafi. [1]

Rayuwar farko da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Odutokun a garin Nsawan, dake kasar Ghana, iyayensa kuma ‘yan kabilar Yarbawa ne dake kasar Nigeria ’yan asalin garin Offa ne, Jihar Kwara kuma suke sana’ar koko . [2] Ya yi kuruciyarsa ya kuma girma a yankin Ashanti amma daga baya mahaifinsa ya koma Najeriya bayan harkar kasuwancinsa ta koko tayi kasa. Bayan kammala karatunsa na Sakandare, ya yi aiki a matsayin magatakarda a Kamfanin Brew[3]eries na Najeriya amma tare da kwazo daga abokansa da suka ga hazakarsa, sai ya nemi izinin shiga Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a shekarar 1972. Ya sauke karatu daga kwalejin tare da digiri na farko da na biyu a Fine Arts a 1975 da 1979. [4] Bayan ya kammala karatunsa na digiri, ya shiga Sashen Fine Arts na ABU a matsayin mataimakin digiri.

  1. Ekpo Udo Udoma. No More Boundaries
  2. ART-NIGERIA: Gani Odutokun Retrospective Hailed in London
  3. Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named :0
  4. Edewor U. Nelson (2015). Gani Odutokun’s Dialogue with Mona Lisa: Interrogating Implications of Euro-African Interface. International Journal of Arts and Humanities. IJAH 4(1), S/No 13