Gaskiya Ta Fi Kwabo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Gaskiya Ta Fi Kwabo
Bayanai
Iri takardar jarida
Harshen amfani Hausa
Tarihi
Ƙirƙira ga Janairu, 1939

Gaskiya Ta Fi Kwabo ( "gaskiya da daraja fiye da kwabo". Kwabo ne "Kashi daya bisa dari" na kuɗin Nijeriya naira) gudan jarida ce a Nijeriya, wadda ake bugata sau uku a mako. Ita ce takarda ta farko da aka fara amfani da ita a harshen Hausa, kuma tana ɗaya daga cikin littattafan farko da ke arewacin Najeriya. Editan Gaskiya Ta Fi Kwabo shi ne Abubakar Imam. A cikin shekara ta alif ɗari tara da arba'in da ɗaya 1941, an ƙara wasu shafuka a cikin Ajami zuwa jaridar ga waɗanda ba sa iya karanta rubutun Roman. An ƙira su ("' Yar Gaskiya").[1]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Adamu, Yusuf M. "Print and Broadcast Media in Northern Nigeria" (pdf). kanoonline.com. Kano Online. Retrieved 2007-08-01.