Gaskiya Ta Fi Kwabo
| Bayanai | |
|---|---|
| Iri | takardar jarida |
| Harshen amfani | Hausa |
| Tarihi | |
| Ƙirƙira | ga Janairu, 1939 |
Gaskiya Ta Fi Kwabo,"gaskiya da daraja fiye da kwabo". Kwabo shi ne "kashi ɗaya bisa dari" na kuɗin Najeriya. Gaskiya ta fi Kwabo gidan jarida ne a Najeriya, wanda ake bugawa tare da wallafawa sau uku a mako. Ita ce takarda ta farko da aka fara amfani da ita a harshen Hausa, kuma tana ɗaya daga cikin littattafan farko da ke arewacin Najeriya. Editan Gaskiya Ta Fi Kwabo shi ne Abubakar Imam. A cikin shekara ta alif ɗari tara da arba'in da ɗaya (1941) an ƙara wasu shafuka a cikin Ajami zuwa jaridar ga waɗanda ba sa iya karanta rubutun Hausar boko. An ƙira su da "Ƴar Gaskiya".[1]
JARIDAR GASKIYA TAFI KWABO
[gyara sashe | gyara masomin]JARIDAR GASKIYA TAFI KWABO
Muhimman bayanai guda sha biyu (12) game da GASKIYA TAFI KWABO.[2]
1. Ita ce jaridar Hausa ta farko a Najeriya.
2. An kirkire ta a shekarar 1939.
3. Ita ce jaridar hausa mafi sanuwa a yammacin Afirka.[3]
4. Ita ce jaridar Hausa ta farko a duniya.
5. Ana buga ta sau uku (3) a sati. Tana fitowa sau uku a sati.[4]
6. Jaridar mallakin gwamnonin arewa a karkashin kamfanin Gaskiya Corporation.[5]
7. Ita ce Jarida ta farko mallakin gwamnati a Najeriya.[6]
8. Ta shahara wurin kawo rahotanni Yakin Duniya Na Biyu II.[7]
9. Babban hedkwatan ta a Zariya.
10. Ita ce jaridar cikin gida mafi jimawa a Najeriya, ta dauki tsawon shekaru saba'in tana aiki.[8]
11. Tana bada gudunmawa wajen gwagwarmayar yada kishin kasa da harshen Hausa.[9]

12. Marubuci Dokta Abubakar Imam ne Editan ta na farko[10]