Jump to content

Gaskiya Ta Fi Kwabo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Gaskiya Ta Fi Kwabo
Bayanai
Iri takardar jarida
Harshen amfani Hausa
Tarihi
Ƙirƙira ga Janairu, 1939

Gaskiya Ta Fi Kwabo,"gaskiya da daraja fiye da kwabo". Kwabo shi ne "kashi ɗaya bisa dari" na kuɗin Najeriya. Gaskiya ta fi Kwabo gidan jarida ne a Najeriya, wanda ake bugawa tare da wallafawa sau uku a mako. Ita ce takarda ta farko da aka fara amfani da ita a harshen Hausa, kuma tana ɗaya daga cikin littattafan farko da ke arewacin Najeriya. Editan Gaskiya Ta Fi Kwabo shi ne Abubakar Imam. A cikin shekara ta alif ɗari tara da arba'in da ɗaya (1941) an ƙara wasu shafuka a cikin Ajami zuwa jaridar ga waɗanda ba sa iya karanta rubutun Hausar boko. An ƙira su da "Ƴar Gaskiya".[1]

JARIDAR GASKIYA TAFI KWABO

[gyara sashe | gyara masomin]

JARIDAR GASKIYA TAFI KWABO

Muhimman bayanai guda sha biyu (12) game da GASKIYA TAFI KWABO.[2]

1. Ita ce jaridar Hausa ta farko a Najeriya.

2. An kirkire ta a shekarar 1939.

3. Ita ce jaridar hausa mafi sanuwa a yammacin Afirka.[3]

4. Ita ce jaridar Hausa ta farko a duniya.

5. Ana buga ta sau uku (3) a sati. Tana fitowa sau uku a sati.[4]

6. Jaridar mallakin gwamnonin arewa a karkashin kamfanin Gaskiya Corporation.[5]

7. Ita ce Jarida ta farko mallakin gwamnati a Najeriya.[6]

8. Ta shahara wurin kawo rahotanni Yakin Duniya Na Biyu II.[7]

9. Babban hedkwatan ta a Zariya.

10. Ita ce jaridar cikin gida mafi jimawa a Najeriya, ta dauki tsawon shekaru saba'in tana aiki.[8]

11. Tana bada gudunmawa wajen gwagwarmayar yada kishin kasa da harshen Hausa.[9]

Jaridar gaskiya

12. Marubuci Dokta Abubakar Imam ne Editan ta na farko[10]

  1. Adamu, Yusuf M. "Print and Broadcast Media in Northern Nigeria" (pdf). kanoonline.com. Kano Online. Retrieved 2007-08-01.
  2. Bbc
  3. Bbc
  4. Bbc
  5. Bbc
  6. bbc
  7. Bbc
  8. Bbc
  9. Bbc
  10. bbc