Jika Dauda Halliru

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Jika Dauda Halliru
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

11 ga Yuni, 2019 -
District: Bauchi Central
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

9 ga Yuni, 2015 - 9 ga Yuni, 2019
District: Bauchi Central
Rayuwa
Cikakken suna Jika Dauda Haliru
Haihuwa 1976 (47/48 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa All Progressives Congress

An haifi Jika Dauda Halliru a shekara ta alif ɗari tara da saba'in da shida 1976 a jihar Bauchi, Nigeria. Dan kasuwa ne kuma dan siyasa. Ya taba zama kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi kuma a yanzu haka dan majalisar dattawa ne mai wakiltar Bauchi ta tsakiya. An fi saninsa da Dokagi.[1][2]

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Ya tafi Kwalejin Tunawa da Sardauna da ke Kaduna, Jihar Kaduna ya kammala a shekara ta alif ɗari tara da casa'in da tara 1999. Daga nan ya koma Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna domin yin karatun Injiniya, kuma ya kammala a shekara ta 2003.

Harkar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

An zabi Jika a matsayin wakilin mazabar Darazo da Ganjuwa a majalisar wakilai ta tarayya kuma ya yi zango biyu a matsayin wakili, na farko tsakanin shekara ta 2007 da shekara ta 2011 da kuma na biyu tsakanin shekara ta 2011 da shekara ta 2015. Sannan a zaben shekara ta 2019 an zabe shi sanata bauchi ta tsakiya karkashin tutar APC.

Rayuwar mutum[gyara sashe | gyara masomin]

Jika musulmi ne. Yayi aure da yara.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

 

  1. Babah, Chinedu (2017-10-04). "JIKA, Hon Dauda Haliru". Biographical Legacy and Research Foundation (in Turanci). Retrieved 2020-02-20.
  2. "Hon. Jika Haliru biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2020-02-20.