Julia Sebutinde

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Julia Sebutinde
Judge of the International Court of Justice (en) Fassara

6 ga Faburairu, 2012 -
Abdul Koroma (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Entebbe (en) Fassara, 28 ga Faburairu, 1954 (70 shekaru)
ƙasa Uganda
Ƙabila Yahudawa
Karatu
Makaranta University of Edinburgh (en) Fassara
Gayaza High School (en) Fassara
Makerere University (en) Fassara
University of Edinburgh School of Law (en) Fassara
Harsuna Turanci
Ibrananci
Sana'a
Sana'a mai shari'a da Lauya
Julia Sebutinde
hoton julia sebutinde

Julia Sebutinde alkaliys ƴar ƙasar Uganda da ke zamanta na biyu a kotun duniya bayan sake zaɓenta da akayi a ranar 12 ga Nuwamba, shekarar 2020. Ita ce kuma shugabar Jami'ar Muteesa I Royal (Muteesa I Royal University) a halin yanzu jami'ar mallakar masarautar Buganda. Ta kasance alkaliya a kotun tun a watan Maris shekarar 2012. Ita ce mace ta farko a Afirka da ta zauna a kotun ICJ.[1][2] Kafin a zaɓe ta a ICJ, Sebutinde ta kasance alkaliya ta Kotun Musamman a Saliyo. An naɗa ta a wannan muƙamin a shekarar 2007.Es dura.

Haihuwa da Tasowar ta[gyara sashe | gyara masomin]

An haife ta a yankin Tsakiyar Uganda mahaifiyar ta ma'aikaciyar gwamnati kuma uwargida mai suna Semambo.Ta halarci Makarantar Firamare ta Lake Victoria a Entebbe a cikin ƙarnin 1960s.[3] Daga nan ta shiga makarantar sakandare ta Gayaza sannan ta koma King’s College Budo, kafin ta shiga jami’ar Makerere ta karanta fannin shari’a. Sebutinde ta kammala karatun digiri a fannin Shari'a (Bachelor of Laws) a shekarar 1977. Ta samu Diploma a fannin Shari'a daga Cibiyar Bunkasa Shari'a da ke Kampala a shekarar 1978. A cikin shekarar 1990, ta yi rajista a Jami'ar Edinburgh don karatun digirin-digirgir a fannin Shari'a (Master of Laws), ta kammala karatunta a shekarar 1991. A cikin 2009, don karrama aikinta da kuma gudummawar da take bayarwa ga adalci na ƙasa da ƙasa, Jami'ar Edinburgh ta ba ta lambar girmamawa ta zama dakta duk dai a fannin Shari'a (Doctor of Law).[4][5]

Tarihin aiki[gyara sashe | gyara masomin]

A Afirka[gyara sashe | gyara masomin]

Julia Sebutinde ta fara aiki a ma'aikatar shari'a a gwamnatin Uganda daga 1978 zuwa 1990. Bayan ta kammala karatunta a Jami'ar Edinburgh a shekarar 1991, ta yi aiki a ma'aikatar Commonwealth a Burtaniya. Daga baya ta shiga ma’aikatar shari’a a jamhuriyar Namibiya, wadda ta samu ƴancin kai a wancan lokacin. A cikin shekarar 1996, an naɗa ta alkaliya a babbar kotun Uganda.A wannan matsayi, ta jagoranci kwamitocin bincike guda uku da suka shafi ma'aikatun gwamnati kamar haka:

  • Cin hanci da rashawa a cikin ƴan sandan Uganda
  • Cin hanci da rashawa a cikin rundunar sojojin Uganda
  • Cin hanci da rashawa a hukumar tattara kuɗaɗen shiga ta Uganda.

A Kotun Musamman a Saliyo[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin 2005 an nada mai shari'a Julia Sebutinde, tare da zama na biyu daga gwamnatin Uganda, zuwa Kotun Musamman a Saliyo, wanda Majalisar Dinkin Duniya ta kafa.Daga baya aka nada ta a matsayin shugabar alkali a kotun sauraron kararrakin zabe II, a wancan lokacin da ke da alhakin sauraron karar da ake yi wa tsohon dan kasar Laberiya, Charles Taylor.A wannan matsayi ta ki halartar zaman ladabtarwa a kan lauyan Taylor, lamarin da ya kai ga rashin da'a na shari'a, amma har yanzu kotun ta musamman ta Saliyo ba ta amince da hakan ba.[6][7]

A Kotun Duniya[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin zaɓen alkalan ICJ, na shekarar 2011.[8] Sebutinde ta kasance ɗaya daga cikin ƴan takara takwas na kujerun shari'a guda biyar a Kotun Duniya. waɗanda ƙungiyoyin ƙasa na Croatia, Denmark, da Uganda suka gabatar da su a cikin Kotun Din-din-din na Arbitration.[9] A zaɓen, ɗan takara mai nasara yana bukatar cikakken rinjayen ƙuri'un a zauren Majalisar Dinkin Duniya da kuma na Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya. A ranar farko da aka kaɗa ƙuri’a an zaɓi ƴan takara huɗu amma ba a cika na biyar ba.[10][11] A lokacin da aka ɗage kaɗa ƙuri'ar, Abdul Koroma, dan takara daga Saliyo, ya samu ƙuri'u 9 daga cikin 15 na Kwamitin Sulhu, da ƙuri'u 8 da ake buƙata don zaɓen. A Majalisar Dinkin Duniya, bayan zagaye biyar na jefa ƙuri'a, Julia Sebutinde, ƴar takarar, ta samu ƙuri'u 97 daga cikin 193, da ƙuri'u 97 da ake buƙata don zaɓe.[12][13] A lokacin da aka ci gaba da kaɗa ƙuri'a a ranar 13 ga watan Disamba, shekarar 2011, Sebutinde ta samu cikakken rinjayen ƙuri'u a kwamitin sulhu da na Majalisar Dinkin Duniya, don haka aka ayyana ta a matsayin zaɓaɓɓiya kuma wadda tayi Nasara a zaɓen.[14]

Waɗansu Muƙaman[gyara sashe | gyara masomin]

Julia Sebutinde ta auri John Bagunywa kuma har yanzu suna tare sun samu ƴaƴa mata biyu. Ana cewa tana matuƙar son kiɗa, ƙwallon ƙafa da kuma iyo. Tana jin daɗin abincin Indiya da abinci mai yaji. Justice Sebutinde ita ce shugabar Jami'ar Kimiyyar Kiwon Lafiya ta Duniya, a Kampala, matsayin da ta riƙe tun 2008.[15]

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Solome Bossa
  • Catherine Bamugemereire
  • Esther Mayambala Kisaakye
  • Jerin shugabannin jami'o'i a Uganda

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Butagira, Tabu (15 December 2011). "Justice Sebutinde Speaks on New World Court Job". Daily Monitor. Retrieved 23 July 2014.
  2. "Julia Sebutinde – First African Woman Sworn in As Judge of UN Court". TheHabariNetwork.Com. Xinhua News Agency. 12 March 2012. Retrieved 23 Juli shekarar 2014. Check date values in: |access-date= (help)
  3. Kalibbala, Gladys (19 August 2008). "Entebbe's Former School of Glory Fades". New Vision. Archived from the original on 9 August 2014. Retrieved 23 July 2014.
  4. TUoE (22 August 2012). "The University of Edinburgh: Honorary Graduates 2008–2009". The University of Edinburgh (TUoE). Retrieved 23 July 2014.
  5. Ssenkaaba, Stephen (29 July 2009). "Justice Sebutinde's Star Still Rising". New Vision. Archived from the original on 8 August 2014. Retrieved 23 July 2014.
  6. Heller, Kevin Jon (27 February 2011). "Judge Refuses to Attend Taylor Lawyer's Disciplinary Hearing". OpinionJuris.Org. Retrieved 23 July 2014.
  7. Sesay, Alpha (2 March 2011). "One Judge Down: Drama Continues At The Charles Taylor Trial". The Guardian. Retrieved 23 July 2014.
  8. "Law School Graduate Nominated for Election to the International Court of Justice". The University of Edinburgh School of Law. 26 October 2011. Archived from the original on 17 June 2013. Retrieved 23 July 2014.
  9. United Nations Secretary-General, . (26 July 2011). "UN Doc. A/66/183–S/2011/453: List of Candidates Nominated By National Groups / Note By the Secretary-General". United Nations. Retrieved 23 July 2014.CS1 maint: numeric names: authors list (link)
  10. United Nations Secretary-General (26 July 2011). "Election of Five Members of The International Court of Justice / Memorandum by The Secretary-General". United Nations. Retrieved 23 July 2014.
  11. IPPF (11 November 2011). "UN Security Council Elects 4 New ICC Judges". International Planned Parenthood Federation (IPPF) Quoting Pan African News Agency (PANA). Retrieved 23 July 2014.
  12. Press Release • UN Security Council• Department of Public Information • News and Media Division (10 November 2011). "SC 6651st–6655th Meetings: Security Council, General Assembly Elect Four New Judges to World Court: Fifth Vacancy Remains to Be Filled, Pending Concurrent Action by Both Bodies". United Nations.
  13. General Assembly/GA/11171/Department of Public Information • News and Media Division • New York, . (10 November 2011). "General Assembly, Concurrently with Security Council, Elects Four Judges to International Court of Justice: Seven Balloting Rounds Fail to Fill Remaining Vacancy on World Court". United Nations. Retrieved 23 July 2014.CS1 maint: numeric names: authors list (link)
  14. United Nations, . (13 December 2011). "Ugandan Judge Elected To Serve on UN World Court". UN News Centre. Retrieved 23 July 2014.CS1 maint: numeric names: authors list (link)
  15. Anthony Bugembe, and Joel Ogwang (3 August 2008). "Health Sciences University Launched". New Vision. Archived from the original on 20 July 2014. Retrieved 23 July 2014.