Justus Esiri
| Rayuwa | |
|---|---|
| Haihuwa |
Abraka (en) |
| ƙasa | Najeriya |
| Mutuwa | 19 ga Faburairu, 2013 |
| Yanayin mutuwa | Sababi na ainihi (Ciwon suga) |
| Ƴan uwa | |
| Yara |
view
|
| Karatu | |
| Matakin karatu | Digiri |
| Harsuna | Turanci |
| Sana'a | |
| Sana'a | jarumi da dan wasan kwaikwayon talabijin |
| Kyaututtuka | |
| Imani | |
| Addini | Kiristanci |
| IMDb | nm2140303 |
Justus Esiri ya kasance gogaggen dan wasan Najeriya wanda ya lashe lambar yabo. An haife shi a ranar 20 ga Nuwamba 1942 kuma ya mutu a ranar 19 ga Fabrairu 2013, yana da shekaru 70, saboda matsalolin ciwon sukari.[1]
Tasowarsa
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Utus a Oria-Abraka, Jihar Delta a ranar 20 ga Nuwamba, 1942. Daga nan ya wuce Effurun ya halarci Kwalejin Urhobo, a Jihar Bendel a lokacin. Ya bar Najeriya zuwa kasar Jamus don yin karatunsa na gaba. Cibiyoyin da ya halarta a Jamus sun haɗa da Jami'ar Maximillan, Munich, Jamusanci (1964), Farfesa Weners Institute of Engineering, West Berlin (1967) da kuma Ahrens School of Performing Arts (1968).[2][3] Yayin da yake nahiyar Turai, ya fara aikin wasan kwaikwayo. Yana aiki a matsayin fassarar Jamusanci ga muryar Najeriya a Jamus, lokacin da ya sami goron gayyata zuwa gida daga gwamnatin Najeriya don yin fim a "The Village Headmaster" wanda ya karba.
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ https://yen.com.gh/60441-20-actors-and-actresses-who-died.html
- ↑ "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-06-28. Retrieved 2023-06-28.
- ↑ "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-06-28. Retrieved 2023-06-28.