Kemi Nelson

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Kemi Nelson
Rayuwa
Haihuwa Lagos, 9 ga Faburairu, 1956
Mutuwa 17 ga Yuli, 2022
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Olukemi Nelson (an haife ta ranar 9 ga watan Fabrairun 1956).[1] 'yar siyasan Najeriya ce kuma mai son mu'amala da jama'a.[2][3] Ita ce Babbar Darakta ta Asusun Kula da Inshorar Jama'a ta Najeriya (NSTIF).[3][4]

Kuruciya da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Nelson a birnin Legas a ranar 9 ga watan Fabrairun 1956 kuma ta halarci Makarantar Grammar Girls na Anglican, Ijebu-Ode inda tayi karatun ta na sakandare. Dangane da karatun ta na jami'a kuwa, ta halarci makarantar koyon aikin jinya a asibitin kwalejin jami’ar Ibadan inda ta cancanci zama ma’aikaciyar jinya/kula da maras lafiya da ungozoma.[5][6] Ta samu digirin MBA a fannin hada-hadar kuɗi da difloma a fannin shari’a daga Jami’ar Jihar Legas Ojo.[6]

Ayyukan siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin 1980s, Nelson ta shiga tsohuwar jam'iyyar National Republican Convention (NRC) a zamanin mulkin Janar Ibrahim Babangida. Ta kasance ‘yar takarar sanata mai wakiltar Legas ta yamma a shekarar 1992 kuma Bola Ahmed Tinubu ya kayar da ita a zaben.[6]

A shekarar 1998, a lokacin mulkin Janar Abacha, ta tsaya takarar Mazaɓar tarayya ta Ikeja a majalisar dokoki. A wannan karon, a matsayin memba na UNCP. Ita ce ta ci zaben amma mutuwar Janar Abacha ta yasa aka watsar da nasarar.[6]

A shekarar 1999 ta shiga kungiyar Alliance for Democracy (AD) sannan daga 1999 zuwa 2003 ta rike kwamishinan harkokin mata da rage radadin talauci na jihar Legas a zamanin Bola Ahmed Tinubu kuma ta rike mukamin shugabar mata na reshen jihar Legas. Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kuma daga baya ta zama shugabar matan Kudu maso Yamma a karkashin jam'iyyar APC.[2]

Ita ce kaɗai mace tilo da ke aiki a Majalisar Shawarar Gwamnan Jihar Legas (GAC).[2]

Ita ce Babbar Daraktar Ayyuka ta Asusun Tallafawa Inshorar wato, "Operations of the Nigeria Social Insurance Trust Fund" (NSITF) kuma a baya ta shugabanci ma’aikatar habakawa, horarwa da samar da ayyukan yi (Ministry of Establishment, Training and Job Creation).[1][7][8]

Rayuwa ta sirri[gyara sashe | gyara masomin]

Tana auren Adeyemi Nelson,[9] darekta mai ritaya na ma’aikatar cikin gida ta tarayya. Sun yi aure a shekara ta 1987 kuma sun haifi 'ya'ya uku tare. An san ta da ƙarancin gashi da take yankewa da kayan kwalliyar gashin ta na musamman.[6][10]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 Ricketts, Olushola. "Again, Kemi Nelson opts for low-key birthday". The Nation.
  2. 2.0 2.1 2.2 Raphael. "Lagos political bigwigs celebrate Kemi Nelson". The Sun (Nigeria).
  3. 3.0 3.1 Akinwale, Funsho. "Kemi Nelson gets federal appointment". The Guardian (Nigeria). Retrieved 9 March 2021.
  4. "Ojekunle, Aderemi (3 August 2019). "31 of the most high-profile female appointees in Buhari's government". Pulse Nigeria. Retrieved 9 March 2021.
  5. "CHIEF (MRS) OLUKEMI NELSON". Pro-Health HMO. Retrieved 6 March 2021.
  6. 6.0 6.1 6.2 6.3 6.4 "Abatti, Tolani (16 February 2016). "Kemi Nelson turns 60, disappoints friends". Encomium. Retrieved 9 March 2021.
  7. Oguntoye, Isaac. "Kemi Nelson marks 64th birthday with close friends". Punch Nigeria.
  8. "Sessou, Aisha (21 March 2019). "Amazing 31 women who made list in President Buhari's second term". Vanguard (Nigeria). Retrieved 12 March 2021.
  9. "When Kemi Nelson's son wedded (2)". Encomium Magazine. 7 December 2013. Retrieved 22 July 2021.
  10. "(Video): Buhari pays special tribute to Kemi Nelson in Aso Rock | Express Day". 26 November 2020. Retrieved 9 March 2021.