Jump to content

Maguzawa

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Maguzawa

[1][2]Maguzawa; mutane ne waɗanda asalinsu Hausawa ne masu bautar Gumaka ko Dodanni ko Rana ko Ɗan-maraƙi ko tsinburbura da dai sauransu. Amma duk da cewa al'ummar Hausawa sun kasance a kan wannan al'ada ta bautar dodanni, sai dai bayan zuwan Addinin Musulunci ƙasashen Hausawa sai suka bar dukkanin waɗancan al'adun kuma sukai watsi dasu.

Hausawa sun rungumi sabon addinin da suka samu sa'annan suka watsar da duk al'adarsu wadda bata dace da Addinin Musulunci ba, amma sai dai an sami wasu daga cikin Hausawan waɗanda basu koma zuwa Musulunci ba tun a waccan lokacin, to sune Hausawan da Musulunci ke kira da Maguzawa, ana kiran namijin da "Bamaguje", mace kuma "Bamagujiya", sannan al'ada da suka ci gaba dabi ta Hausawa, ana kiranta da "Maguzanci".

[3][4]Har wayau, ana samun Maguzawa a ko'ina a ƙasashen Hausa sai dai basu cika zama cikin mutane ba, wannan ko ya faru ne saboda irin tsangwama da ake yi musu tun a waccan lokacin da suka ƙi su koma Addinin Musulunci, yaƙarsu da Hausawa Musulmi ke yi, shi ya sa suke zama a bayan gari. Sun dogara ne a kan yin noma da kiwo, mafiya yawan Maguzawa ba su da ilimin zamani, domin dodanninsu ba za su yarda su nemi wani ilimi ba. Su dai Maguzawa mutane ne Hausawa da yawancinsu manoma ne, kuma suke a ƙauyukan ƙasar Hausa.

Malam Ibrahim ya ce mutane ne masu ƙwazo da ƙoƙari, sai dai yawancinsu ba Addinin Musulunci suke bi ba, kamar wadanda suke tare da su a yankunan da suke, amma daga baya sannu a hankali wasu daga cikinsu na shiga Musulunci.

Ya ƙara da cewa al'adunsu da yarensu, da kuma sutura sun dace da Hausawa musamman kafin Jihadin Shehu Ɗanfodio. Hausawa musamman a lokacin jihadin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo suna nan birjik a wurare da dama musamman kamar wasu ƙauyuka a ƙasar Kano da ma Katsina. Abin da aka fi karkata a kai na tarihi a cewar masanin shi ne mutane ne waɗanda suka zo daga Habasha tun ana ƙiransu Majusu, suka riƙa sauya suna har aka dawo ana kiransu da Maguzawa.

Da yawan masu tarihi na ganin cewa su ne asalin Hausawa, daga baya suka ilimantu suka zama Hausawan da aka sani a yanzu. To amma ya ce daga baya an samu ƙaulani, domin wasu na ganin cewa alama ta fi nuna cewa mutanen Afrika ta arewa ne, domin al'adar da ta fito daga nan irin tasu ce, kafin su dawo arewacin nahiyar ( Afrika). Akwai mutanen da suka zo daga Habasha suka zauna a Dutsen Dala da ke Kano, kuma mashahurin sarkinsu shi ne Barbushe, waɗannan mutane sun rika bautar gumaka, su kuwa Maguzawa da aka sani a yanzu ba sa bautar gumaka, amma suna da nasu abubuwan na tsaface-tsaface.

Asalin Maguzawa da alakarsu da Hausawa

[gyara sashe | gyara masomin]

Mutane da dama sun dade suna da wata tambaya a zuciyarsu a kan su waye Maguzawa?[5]

A wannan labarin BBC Hausa ta bayyana ko su waye Maguzawa kamar yadda wani marubuci kuma manazarci Ibrahim Aminu Daniya ya labarta mana. Su dai Maguzawa mutane ne Hausawa da yawancinsu manoma ne kuma suke a ƙauyukan ƙasar Hausa.BMalam Ibrahim ya ce mutane ne masu ƙwazo da ƙoƙari, sai dai yawancinsu ba Addinin Musulunci suke bi ba, kamar wadanda suke tare da su a yankunan da suke, amma daga baya sannu a hankali wasu daga cikinsu na shiga Musulunci. Ya ƙara da cewa al'adunsu da yarensu, da kuma sutura sun dace da na Hausawa musamman kafin Jihadin Shehu Danfodio, kuma suna nan birjik a wurare da dama musamman kamar wasu ƙauyuka a ƙasar Kano da ma Katsina. Abin da aka fi karkata a kai na tarihi a cewar masanin shi ne mutane ne wadanda suka zo daga Habasha tun ana kiransu Majusu, suka riƙa sauya suna har aka dawo ana kiransu Maguzawa. Da yawan masu tarihi na ganin cewa su ne asalin Hausawa daga baya suka ilimantu suka zama Hausawan da aka sani a yanzu. To amma ya ce daga baya an samu kaulani, domin wasu na ganin cewa alama ta fi nuna cewa mutanen Afrika ta arewa ne, domin al'adar da ta fito daga nan irin tasu ce, kafin su dawo arewacin Afrika.[5]

"Akwai mutanen da suka zo daga Habasha suka zauna a Dutsen Dala da ke Kano, kuma mashahurin sarkinsu shi ne Barbushe, wadannan mutane sun rika bautar gumaka, su kuwa Maguzawa da aka sani a yanzu ba sa bautar gumaka, amma suna da nasu abubuwan na tsaface-tsaface."[5]

Har yanzu dai ba a san Maguzawa da wani harshe ba in ba Hausa ba.[4]

  • Mahangar kimiyya da addini kan bangon duniya
  • Yadda ilimin lissafi ya samo asali daga ɗakin karatu na Musulunci
  • Abubuwan da suka kamata ku sani game da amfanin gashi a jikin dan Adam

Inda aka fi samun su

[gyara sashe | gyara masomin]

Masanin ya ce an fi samun Maguzawa ne a kasar Hausa musamman ma a dazukan Kano da Katsina, akwai su suna nan amma sannu a hankali suna shiga cikin jama'a suna karbar Musulunci, don haka yanzu ƙalilan ne suka rage daga cikinsu. Ya ce wasu daga cikin al'adunsu da suka yi kama da na Hausawan da suka rungumi Musulunci a yanzu sun hada da na bukukuwan aure ko na mutuwa da kaɗe-kaɗe da raye-raye.[2]

"Sunayensu sun sha bambam da na Hausawan yanzu, domin su suna sanya sunaye ne dai-dai da yanayi ko lokaci.[3]

Misali idan yanayin roron wake ne sai su ce 'Ci Wake,' ko idan lokacin damina ne sai su sa wa yaro suna 'Damina,' ko su sanya sunayen aljanu saboda su ne abokan mu'amalarsu musamman wajen bori da sauransu.[4]

Marubucin ya ci gaba da cewa a yanzu dai babu wani ƙiyasi na yawan Maguzawan da suka rage a kasar Hausa, abin da kawai yake a fili shi ne yawansu ya ragu, kuma yana ci gaba da raguwa domin yawanci sun hade da sauran jama'a yadda in ba sun faɗa ba, ba za ka gane ba, don haka akwai yiwuwar watarana ma za su kare ɗungurungum.[5]


https://bbchausa.com

A cewar Tarihi, Maguzawa sune haƙiƙanin asalin tsatson Hausawa. An ambaci cewar Maguzawa sun kasance acikin Kano tun farkon zamanin Kano sama da shekaru dubu da suka gabata. Bambance-bambancen Maguzawa da sauran al’ummar Kano ya faro ne tun a karni na 14 a zamanin mulkin Yaji I wanda da hadin kan Malaman Wangara suka yi nasarar cusa Imani da addinin Musulunci ga mutanen Kano. A yayin da addinin Musulunci ya ci gaba da rikidewa zuwa wani nau'i me kama da camfi wanda Jihadin Fulani ke kokarin kawar dashi, sai Maguzawa da addininsu suka rarrabu a Jihar. Sun yi riko da mafi dadewa nau'in maguzanci ne kawai yayin da sarakunan Hausawa na Kano da mafi yawan mabiyansu suka yi wani tsari na Musulunci wanda ya hada da abubuwa daga maguzanci. Misali daya daga cikin abubuwan da ake girmamawa a Kano kafin Jihadi, akwai Alqur'ani da aka lullube da fatar akuya ko saniya mai suna "Dirki". Su ma sarakunan Hausawa sun san suna da ’yan iska da malaman addinin Musulunci da za su yi kira a lokacin da suke bukata. Duk da haka, yayin da aka samu bambance-bambance tsakanin ayyukan Maguzawa da tsarin Musulunci na gaba daya da ake yi a wadannan jahohin, Maguzawa ya kasance wani bangare mai matukar muhimmanci a jihar, kuma sau taru sarakunan Hausawa suna kiransu domin su aiwatar da ayyukan tsafi agaresu. Kadan ne daga cikin Maguzawa suka rage a yanzu yayin da Mafi yawansu suka musulunta, wasu tsiraru kuma suka koma Kiristanci. [ <span title="This claim needs references to reliable sources. (August 2022)">abubuwan da ake bukata</span> ]