Masarautar Kontagora

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Masarautar Kontagora

Wuri
Map
 10°24′N 5°28′E / 10.4°N 5.47°E / 10.4; 5.47
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaJihar Neja

Masarautar Kontagora jiha ce ta gargajiya wacce ke dauke babban birnin Kontagora, Jihar Neja, a Nijeriya.[1][2] Masarautar Kontagora tana cikin manyan masarautun jihar Neja kamar Masarautar Kagara, Masarautar Suleja da sauransu.

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

Kontagora yanki ne wanda asalinsa ya rabu tsakanin ƙananan masarautu daban-daban (Aguarra, Dakka-Karri, Kambari, Dukawa, da Ngaski) wanda mutanen Fula suka ci su da yaƙi a tsakanishekarar n 1858 zuwa 1864, suka koma masarautar Kontagora, abin dogaro ga Daular Sokoto.[3][4]

Bayan wani hari da makami, tun daga ranar 31 ga watan Janairun shekarar 1901, Masarautar ta faɗa ƙarƙashin mulkin Birtaniya, inda kuma ta zama lardi na farko a cikin yankin Arewacin Najeriya na Birtaniyya sannan kuma a ƙarƙashin Turawan mulkin mallaka na Najeriya, har zuwa lokacin samun ‘yancin kan kai a shekarar 1960 da ƙasar ta samu.[5][6][7]

A yanzu dai Kontagora ta ƙunshi masarautun Kontagora mai ɗauke da masarautun Wushishi, da yankunan Sarkin Bauchi, da masarautar Kagara, duk a ƙarƙashin mulkinsu sun haɗe zuwa kananan hukumomin Mariga, Magama, da Rafi.[8]

Jerin sarakunan[gyara sashe | gyara masomin]

Sunayen sarakuna da lokutan zamanin mulkinsu da aka naƙalto daga; John Stewart's African States and Rulers (1989).[9]

Sarakunan Sudan of the Kontagora Emirate
No. Suna Fara mulki Ƙarshen sarauta
1 Umaru Nagwamatse 1864 1876
2 Abubakar Modibbo 1876 1880
3 Ibrahim Nagwamatse 1880 1901
ba a gane ba 1901 Afrilu 1903
3 Ibrahim Nagwamatse Afrilu 1903 26 Oktoba 1929
4 Umaru Maidubu 26 Oktoba 1929 Fabrairu 1961
5 Mu'azu Fabrairu 1961 1976
6 Al-Hajji Saidu Namaska 1976 7 Satumba 2021[10]
7 Muhammad Bara'u Mu'azu II Oktoba 7, 2021[11] har zuwa yau

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. SALAMONE, FRANK A. (1976), "Religious Change in a Northern Nigerian Emirate", The Realm of the Extra-Human, DE GRUYTER MOUTON, doi:10.1515/9783110805840.123, ISBN 978-3-11-080584-0
  2. "King-Lists, Chronicles and Other Minor Historical Works: Kontagora". Arabic Literature of Africa Online. doi:10.1163/2405-4453_alao_com_ala_20014_26.
  3. Brizvela-Garcia, Esperanza (2005-04-07), "Sokoto Caliphate", African American Studies Center, Oxford University Press, doi:10.1093/acref/9780195301731.013.43439, ISBN 978-0-19-530173-1
  4. Last, Murray. (1977). The Sokoto caliphate. Longman. OCLC 473688413.
  5. Brizvela-Garcia, Esperanza (2005-04-07), "Sokoto Caliphate", African American Studies Center, Oxford University Press, doi:10.1093/acref/9780195301731.013.43439, ISBN 978-0-19-530173-1
  6. Falola, Toyin; Tibenderana, P. K. (1991). "Sokoto Province under British Rule 1903-1939". The International Journal of African Historical Studies. 24 (1): 183. doi:10.2307/220113. ISSN 0361-7882. JSTOR 220113.
  7. July, Robert William (1998). A history of the African people. ISBN 0-88133-980-6. OCLC 43811431.
  8. Northern Nigerian Survey. (1966), Kontagora, Northern Nigerian Survey, OCLC 5568935
  9. Stewart, John (1989). African States and Rulers. London: McFarland. p. 154. ISBN 0-89950-390-X.
  10. "emir-kontagora-alhaji-namaska-dead". prnigeria.com. 7 September 2021. Retrieved 30 October 2021.
  11. Ahmadu Maishanu, Abubakar (7 October 2021). "Niger State Government announced Muhammad Barau as the seventh Emir of Kontagora". premiumtimesng.com. Retrieved 30 October 2021.