Surame

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Surame


Wuri
Map
 13°05′15″N 4°53′55″E / 13.0875°N 4.8986°E / 13.0875; 4.8986
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaKebbi
Katangar tsohuwar birni a cikin Surame

Tsohon birnin Surame wani abin tarihi ne na al'ummar Najeriya dake cikin jihar Sokoto dake arewa maso yammacin Najeriya. Muhammadu Kanta Sarkin Kebbi ne ya ƙirƙiro tsohon birnin a ƙarni na 16, wanda ya mallaki daula a yankin. An bar garin a kusan a shekarar 1700 lokacin da babban birnin, birnin garin ya koma Birnin Kebbi.[1]

Bayani[gyara sashe | gyara masomin]

Birnin na ya mamaye yanki kimanin kilomita 9 km, wurin ya ƙunshi harsashin ginin matsugunan mutane, ganuwa, rijiyoyi da tukwane.[2] Akwai katangar tsaro da aka gina daga dutse a kusa da ƙauyuka, da kuma ramuka da aka haƙa a kusa da babban yanki kuma an cika su da ciyayi masu ƙaya a matsayin wata hanyar kariya ko tsaro.

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

Tsohuwar Masarautar Suram tana da iko daga ƙarni na 15 zuwa na 16.[2]

Kayan tarihi na Nijeriya[gyara sashe | gyara masomin]

An ayyana Surame a matsayin daɗaɗen abin tarihi na ƙasa a ranar 15 ga watan Agustan shekarar 1964.[1]

Matsayin Al'adun Duniya[gyara sashe | gyara masomin]

Birnin an saka sunansa cikin jerin abubuwan tarihi na UNESCO a ranar 8 ga watan Oktoban shekarar 2007 a ɓangaren rukunin kayan tarihi na (Mixed Cultural + Natural)--->( Al'adun da aka cakuɗe wuri ɗaya da na asali).[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 "NATIONAL COMMISSION FOR MUSEUMS AND MONUMENTS". NATIONAL COMMISSION FOR MUSEUMS AND MONUMENTS. Archived from the original on 25 February 2012. Retrieved 29 April 2012.
  2. 2.0 2.1 2.2 Surame Cultural Landscape - UNESCO World Heritage Centre