Taron kasa da kasa na Calabar kan Adabin Afirka da Harshen Turanci

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Taron kasa da kasa na Calabar kan Adabin Afirka da Harshen Turanci
Taron kasa da kasa na Calabar kan Adabin Afirka da Harshen Turanci

ICALEL taƙaitaccen bayani ne na taron kasa da kasa na Calabar akan adabin Afirka da Harshen Ingilishi wanda masanin Afirka kuma mai suka Ernest Emenyonu ya kafa kuma ya jagoranta.[1] A tsakiyar taron akwai marubutan Afirka da masu suka daga sassan duniya. Taron farko mai taken "Mace a matsayin Marubuciya a Afirka" an gudanar da shi a dakin taro na Jami'ar Calabar[2] a watan Mayun 1981 kuma marubuciyar Ghana Ama Ata Aidoo ita ce babbar mai jawabi. Jigogin 1982, wato "Littattafai a Harsunan Afirka" da "Rubutun Littattafai don Yara", sun nuna Ngũgĩ wa Thiong'o da Bessie Head a matsayin masu magana.[3] Manyan marubutan Afirka da suka yi fice a wajen taron a tsawon shekaru sun hada da Cyprian Ekwensi, Chinua Achebe, Wole Soyinka, Chinweizu, Dennis Brutus, Buchi Emecheta, Flora Nwapa, Elechi Amadi, Ken Saro Wiwa, Chukwuemeka Ike, Nuruddin Farah, Syl Cheney -Coker, kaɗan da a ka ambata.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. E. N. Emenyonu, "Introduction", Goatskin Bags and Wisdom: New Critical Perspectives on African Literature , Trenton: AWP, 2000. ISBN 0-86543-670-3 (hb), ISBN 0-86543-671-1 (pb)
  2. University of Calabar https://www.unical.edu.ng › event-2... University Of Calabar Nigeria - Event
  3. Times of India https://timesofindia.indiatimes.com › ... Calabar International Conference On African Literature And The ...