Abla al-Kahlawi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abla al-Kahlawi
Rayuwa
Cikakken suna عبلة مُحمَّد مرسي عبد اللطيف الكحلاوي
Haihuwa Kairo, 15 Disamba 1948
ƙasa Kingdom of Egypt (en) Fassara
Republic of Egypt (en) Fassara
United Arab Republic (en) Fassara
Misra
Harshen uwa Larabci
Mutuwa Kairo, 24 ga Janairu, 2021
Yanayin mutuwa Sababi na ainihi (Koronavirus 2019)
Ƴan uwa
Mahaifi Mohammed Al Kahlawi
Karatu
Makaranta Jami'ar Al-Azhar
Harsuna Larabci
Sana'a
Sana'a university teacher (en) Fassara, philanthropist (en) Fassara, dawah (en) Fassara da marubuci
Employers Jami'ar Al-Azhar
Umm al-Qura University (en) Fassara
Mamba Q12239072 Fassara
Imani
Addini Musulunci

Abla al-Kahlawi (15 Disamba 1948 - 25 Janairu shekarar 2021) malamar Masar ne kuma malamar fikihu, haka nan kuma shugabar addini, mai wa'azi, kuma mai gabatar da talabijin. Tayi koyarwa a jami'ar Al Azhar da ke birnin Alkahira na kasar Masar , inda ta kasance shugabar tsangayar ilimin addinin musulunci da na larabci a kwalejin mata. An jera ta acikin bugu na farko na Musulmai 500 masu tasiri a kan harkokin addini da mata, a shekarar 2009, kuma tayi ta yada labaran mata da fikihu. Tayi wa'azi a Masar, kai tsaye da ta talabijin, da kuma Saudiyya, kuma tayi wa'azi kowace rana tsawon shekaru biyu a Masallacin Harami, Masallacin Musulunci mafi muhimmanci a Saudiyya, tsakanin shekara ta1987 zuwa shekara ta 1989.

Rayuwarta[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Abla al-Kahlawi a ranar 15 ga Disamba shekara ta 1948 a Masar. Mahaifinta, Mohammed al-Kahlawi shahararren mawakin nauheed ne. Ta mutu tana da shekaru 72, na COVID-19.

Sana'arta[gyara sashe | gyara masomin]

Al-Kahlawi tayi karatun shari'ar Musulunci a jami'ar Azhar dake birnin Alkahira na kasar Masar inda ya samu digiri na biyu a shekarar 1974 sannan tayi digiri na uku a shekarar 1978 a fannin. A shekarar 1979 aka nada ta shugabar sashen shari’a a tsangayar ilimi a kwalejin mata dake Makkah. Daga baya aka nada ta shugabar ilimin addinin musulunci da na larabci a kwalejin mata ta jami'ar Azhar. Ta kuma koyar a Kwalejin Ilimin ‘Yan Mata da ke Riyadh a kasar Saudiyya.

Daga shekara ta1987 zuwa shekara ta 1989, al-Kahlawi tanayin wa'azi kullum a Masallacin Harami, masallaci mafi muhimmanci na Musulunci, dake kasar Saudiyya. Darussanta sun samu halartar alhazai mata daga sassan duniya. Ta cigaba dayi wa mata wa'azi akasar Masar bayan haka, a wasu mashahuran masallatai da suka hada da Masallacin Azhar, al-Hamd, da Al-Hossari, da kuma wani masallaci da mahaifinta ya kafa, awajen addu'o'in da jama'a suka halarta. Ta kuma gabatar da shirye-shiryen addini da dama na yankin da jama'a ke kallo, kuma masu sauraronta sunfi saninta da 'Mama Abla'. [1] Karatuttukan Al-Kahlawi sun kunshi jawabai kan shari'a da ka'idojin Musulunci, da bayanin nassoshin addini, da amsa tambayoyi kan fikihu. A cewar Oxford Encyclopedia of Islam and Women, karatunta da wa'azin da tayi "....tayi sukane ga fassarar misogynistic na nassoshin Musulunci da yunƙurin rage ɗabi'a zuwa ga tsattsauran ra'ayi," yayin da kuma ke bada shawarar haƙƙin mata na saki, tare da ƙarfafa dabi'un " ...haƙuri, daidaitawa, tausayi, da zaman lafiya." [1]

A cikin shekara ta 2009, an saka ta amatsayin ɗaya daga cikin Musulmai 500 Mafi Tasiri, wanda shine bugu na farko na jerin shekara da Cibiyar Nazarin Dabarun Islama ta Masarautar dake Jordan ta ƙirƙira, kuma tana ba da kowace shekara tare da haɗin gwiwar Cibiyar Yarima Al-Waleed Bin Talal ta Muslim. - Fahimtar Kirista a Jami'ar Georgetown a Amurka . A jerin sunayen da aka ambata ta amatsayin "...babbar hukuma a kan al'amurran da suka shafi na musamman ga mata, kuma shugabar daya daga cikin mafi kyau girmamawa ga scholarships mata musulmi a duniya." [2] Littafin nan na Oxford Encyclopedia of Islam and Women ya bayyana ta da cewa "... daga cikin manyan mashahuran limaman mata (malaman Musulunci) a kasashen Larabawa."

A shekara ta 2006, ta kasance ɗaya daga cikin gungun fitattun jagorori da malamai arba'in da Daya 41 na Musulunci waɗanda suka rubuta don yin Allah wadai da tashe-tashen hankula da suka biyo bayan rigimar zane-zane na <i id="mwPg">Jyllands-Posten</i> Muhammad, yayin da a lokaci guda sukayi watsi da zane-zanen da kansu. Ta kasance daya daga cikin wadanda suka rattaba hannu kan A Common Word Tsakanin Mu da Kai, wata budaddiyar wasika da shugabannin addinin Musulunci sukayi aike zuwa ga shugabannin addinin Kirista, suna kira ga zaman lafiya tsakanin addinan biyu. Aikinta na wa'azi ta samu karbuwa daga Entissar Amer, uwargidan shugaban kasar Masar, wacce ta bayyana aikinta a matsayin "....take mai daraja da ban mamaki akan hanyar sadaka da wa'azi."

A Masar, al-Kahlawi ta kafa wata babbar kungiyar agaji a Mokattam, Alkahira, don ba da agaji ga marayu, da kuma mutanen dake fama da cutar kansa da cutar Alzheimer.

Labarai[gyara sashe | gyara masomin]

Al-Kahlawy ta rubuta fitattun littafai da dama kan fikihu. Waɗannan sun haɗa da:

  • Fa'lyat al-Zakāt fi Himayat al-Iqtisad wa al-Tanmiya ( The Importance of Alms in Securing Economy and Development, 1996)
  • Al-Marā bayn Tahārat al- Bātin wa al-Zāhir ( Women: The Inside and Outside Sanctity, 1997)
  • Qaday al-Mar ʾ a fi al-Hajj wa-al- 'Umra

Nassoshi[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named :2
  2. Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named :4