Daniel Akintonde

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Daniel Akintonde
Gwamnan jahar ogun

9 Disamba 1993 - 22 ga Augusta, 1996
Olusegun Osoba - Sam Ewang (en) Fassara
Rayuwa
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Yarbanci
Karatu
Makaranta Jami'ar Tsaron Nijeriya
Harsuna Turanci
Yarbanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da soja

Kanar Daniel Akintonde (an haife shi ranar 21 ga watan Nuwamban 1949) a Jihar Filato. Ya fito ne daga Ogbomoso dake Jihar Oyo.[1] An naɗa shi gwamnan soja a jihar Ogun ta Najeriya daga cikin watan Disambar 1993 zuwa watan Agustan 1996 a lokacin mulkin soja na Janar Sani Abacha.[2][3]

A 1994 Akintonde ya canza sunan Kwalejin Ilimi ta Jihar Ogun zuwa Kwalejin Ilimi ta Tai Solarin don girmama marigayi likita Tai Solarin.[4] Akintonde na daga cikin waɗanda aka kama da hannu a juyin mulkin watan Disamba na shekarar 1997.[5] An wanke shi daga tuhumar a ranar 20 ga watan Afrilun 1998.[6]

Ya yi ritaya daga aikin soja a cikin watan Yunin 1999, tare da dukkan jami’an da suka taɓa riƙe muƙamin minista, gwamnoni ko masu mulki a zamanin gwamnatin Babangida, Abacha da Abubakar.[7] A cikin watan Agustan 1999 ne Majalisar Dokokin Jihar Ogun ta gayyaci Akintonde domin ya amsa tambayoyi kan wasu kwangiloli da aka bayar a lokacin da yake mulki. An hana ƴan jarida shiga sauraron ƙarar.[8]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-02-03. Retrieved 2023-03-28.
  2. https://www.worldstatesmen.org/Nigeria_federal_states.htm
  3. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2022-08-10. Retrieved 2023-03-28.
  4. https://web.archive.org/web/20090625043236/http://www.tasuedu.org/tasuedweb/elibrary/docstore/TASUEDpub/Student%20Handbook
  5. https://www.unhcr.org/refworld/topic,4565c2252c,4565c25f389,3ae6ad056c,0.html
  6. http://www.unhcr.org/refworld/pdfid/3ae6a6924.pdf
  7. https://www.yahoo.com/
  8. https://web.archive.org/web/20110723204943/http://www.mediarightsagenda.net/other%20publications/Annuall%20Report%20for%201999.pdf