Garba Shehu
3 ga Yuni, 2003 - | |||
| Rayuwa | |||
| ƙasa | Najeriya | ||
| Sana'a | |||
| Sana'a | ɗan siyasa | ||
| Imani | |||
| Jam'iyar siyasa | Peoples Democratic Party | ||
|
|
Wannan mukalar bata da Reference (Manazarta) ko daya, ka taimaka ta hanyar samar da Manazarta daga littafi ko yanar gizo, duba wannan shafin domin samun masaniya akan yanda zaka samar da Reference (Manazarta) a cikin wannan mukalar.
|
Mallam Garba Shehu (an haifeshi ranar 27 ga watan Nuwamba shekara ta alif dari tara da hamsin da tara miladiyya 1959) ɗan Jarida ne kuma ɗan siyasa ne wanda ya kasance a matsayin Babban Mataimaki na Musamman kan Yaɗa Labarai ga tsohon Shugaban Tarayyar Najeriya, Muhammadu Buhari. [1] Ya kasance shugaban ƙungiyar Editocin Najeriya kuma yayi magana game da tsohon mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Atiku Abubakar.[2][3]
Bayanan Fage
[gyara sashe | gyara masomin]An haife shine a garin Dutse, jihar Jigawa. Kuma ya taso ne tare da iyayensa duka a jihar ta Jigawa.[4]
Ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]Shehu ya halarci makarantar firamare ta Dutse a shekarar alif ɗari tara da saba'in, 1970. Daga nan ya wuce Kwalejin Barewa, Zariya a shekara ta alif ɗari tara da saba'in da biyar, 1975. Acikin shekara ta alif ɗari tara da da tamanin da ɗaya, 1981, ya sami Digiri na farko a Jami’ar Bayero. Kano.[5]
Ayyuka
[gyara sashe | gyara masomin]Shehu ya fara aikin sa ne a matsayin wakili a Gidan Talabijin na Najeriya, Sakkwato acikin shekara ta 1982. Sannan ya kasance wakilin labarai na makamashi a Network News Lagos a cikin shekara ta 1984. [6]Ya yi aiki a matsayin Shugaban Editocin Guild na Najeriya, shi ne darekta a lokacin Media da Publicity na Dukkanin 'yan majalissun ci gaban yakin neman zaben shugaban kasa acikin shekara ta 2015. Acikin shekarar 2015, [7]shugaban tarayyar Najeriya Muhammad Buhari, ya nada shi a matsayin babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai da yada labarai kuma yanzu haka yana rubutu a matsayin jaridar Premium Times ta Najeriya.[8][9]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "Buhari appoints Garba Shehu, Femi Adesina as spokesmen | Premium Times Nigeria". 2015-05-31. Retrieved 2020-10-14.
- ↑ "Garba Shehu: A quintessential presidential spokesman". Vanguard News. 2017-11-27. Retrieved 2020-10-14.
- ↑ Garba Shehu: I'm a Driver's Son...I Wasn't Born with a Silver Spoon, I Worked Hard to Propel Myself". THISDAYLIVE. 2019-08-31. Retrieved 2020-10-14.
- ↑ Nwabueze, Chinenye. "Garba Shehu biography, early life, marriage, education – MassMediaNG". Retrieved 2020-10-14.
- ↑ Nwabueze, Chinenye. "Garba Shehu biography, early life, marriage, education – MassMediaNG". Retrieved 2020-10-14.
- ↑ "Who is Garba Shehu? Biography, Education, Marriage and Politics". Lanre News. 2021-05-04. Retrieved 2021-05-04.
- ↑ "Who is Garba Shehu? Biography, Education, Marriage and Politics". Lanre News. 2021-05-04. Retrieved 2021-05-04.
- ↑ "Garba Shehu at 60: A tribute". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News. 2019-11-27. Retrieved 2020-10-14.
- ↑ Nwabueze, Chinenye. "Garba Shehu biography, early life, marriage, education – MassMediaNG". Retrieved 2020-10-14.