Hameem Nuhu Sanusi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Hameem Nuhu Sanusi
Rayuwa
Sana'a

Muhammad Hameem Nuhu Sunusi CFR (an haife shi a ranar 26 ga Fabrairu, 1979), sarkin Najeriya ne wanda yake rike da sarautar Dutse, babban birnin jihar Jigawa a Arewacin Najeriya. Ya yi shekarunsa na farko a jihar Kano kafin ya koma Jigawa a shekarar 1995, bayan hawan mahaifinsa kan mukamin Sarkin Dutse.[1][2][3][4][5][6]

Rayuwar farko da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Muhammad Hameem Nuhu Sunusi ya fara tattakin karatunsa ne a Kano, inda ya halarci makarantar Kano Capital, sannan ya halarci makarantar firamare ta Airforce inda ya yi karatunsa na reno da firamare. Ya ci gaba da karatunsa na sakandire a Crescent International, sannan ya kammala karatunsa a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Kano. Bayan kammala karatunsa na farko, ya yi karatu a kasashen waje, inda ya samu digiri na farko da na biyu a jami'ar Malaysia. A shekarar 2006 ya kamalla hidimar bautar kasa (NYSC) a majalisar kasa da ke Abuja bayan ya dawo Najeriya.[7] Ya rike mukamin Dan Iyan Dutse kafin ya zama sarki a shekarar 2023. Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba shi lambar yabo ta Kwamandan Tarayyar Tarayya (CFR) a ranar 28 ga Mayu 2023.

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Muhammad Hameem Nuhu Sunusi ya fara sana’ar kasuwanci tun da farko amma daga baya ya koma bangaren injiniyanci, sha’awar da ya dade. Ya kasance shugaban ci gaban kasuwanci a Bilyak Consulting daga 2007 zuwa 2011. Ya kuma yi aiki da SMD Consulting daga 2011 zuwa 2016 a matsayin Shugaban yankin Arewa kafin daga bisani ya zama Manajan Darakta na HMS Energies Limited.

Magana[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Wane ne sabon sarkin Dutse?". BBC News Hausa. 2023-02-05. Retrieved 2023-10-14.
  2. Usman, Mustapha (2023-02-05). "Hameem Nuhu emerges new Emir of Dutse". Daily Nigerian (in Turanci). Retrieved 2023-10-14.
  3. Nigeria, Guardian (2023-02-06). "Muhammad Hameem named new Emir of Dutse". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). Retrieved 2023-10-14.
  4. "An nada sabon sarkin Dutse da ke Jaigawa – DW – 02/05/2023". dw.com. Retrieved 2023-10-14.
  5. "Gwamnan Jigawa ya amince da nadin Muhammad Hameem Nuhu Sanusi a matsayin sabon Sarkin Dutse". RFI. 2023-02-05. Retrieved 2023-10-14.
  6. Hassan, Rabiu Sani (2023-02-05). "Muhammad Hameem ya zama Sarkin Dutse". PRNigeria Hausa (in Turanci). Retrieved 2023-10-14.
  7. "HM, Dr. Muhammad Nuhu Sanusi, Emir of Dutse". Naturenews.africa (in Turanci). Archived from the original on 2023-10-07. Retrieved 2023-10-14.