Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa
Bayanai
Iri government agency (en) Fassara da law enforcement agency (en) Fassara
Ƙasa Najeriya
Aiki
Mamba na International Association of Anti-Corruption Authorities (en) Fassara
Tarihi
Ƙirƙira 2003

efcc.gov.ng


Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) wata hukuma ce mai tabbatar da doka a Najeriya da ke binciken laifukan kuɗi, kamar zamba (damfara 419) da kuma karkatar da kuɗaɗe, ba bisa ƙa'ida ba.[1] An kafa hukumar EFCC ne a shekarar 2003, a matsayin wani ɓangare na martanin matsin lamba daga Hukumar Yaƙi da Safarar Kuɗaɗen Haram (FATF),[2] wadda ta bayyana Najeriya a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashe 23 da ba su da haɗin kai a ƙoƙarin da ƙasashen duniya ke yi na yaƙi da safarar kuɗaɗen haram.[1] Hukumar tana da babban ofishinta a Abuja, babban birnin Najeriya.

Jami’an rundunar shiyyar Benin na hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa, EFCC, sun kama wani Irabor Kennedy Osasogie bisa zargin zamba.[3][4]

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin ƙasar, zagon ƙasa, EFCC, ta jera abubuwan da ake buƙata don samun nasarar shiga kasuwar gwanjon kadarorin da ke faɗin ƙasar nan, waɗanda ke ƙarƙashin dokar hana almundahana.[3]

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

A ƙarƙashin tsohon shugaban hukumar EFCC Nuhu Ribadu, hukumar ta yi maganin almundahanar kudi ta hanyar gurfanar da wasu manyan mutane da ake zargi da cin hanci da rashawa, tun daga tsohon babban jami’in tsaro na Najeriya zuwa wasu shugabannin bankuna da dama. A shekarar 2005, EFCC ta kama jami’an gwamnati da suka hada da, Diepreye Alamieyeseigha.[5]

A watan Satumban 2006, EFCC na binciken gwamnoni 31 daga cikin gwamnonin jihohi 36 dake a tarayyar Najeriya akan zargin almundahana.[6] A watan Disambar 2007, gwamnatin tarayyar Najeriya, bayan bincike mai zurfi da EFCC da wasu ƙungiyoyi suka yi, ta wanke ƴan’uwan Vaswani[7] daga duk wani laifi kuma ta gayyace su su dawo cikin ƙasar. Jaridun Najeriya mai suna "This Day" da wasu manyan jaridun ƙasar sun ruwaito gaskiyar takardar amincewarsu inda suke nakalto rubutu daga umarnin da FG ta bayar. A watan Afrilun 2008 ne hukumar EFCC ta fara bincike kan ƴar tsohon shugaban Sanatoci a Najeriya, Iyabo Obasanjo-Bello kan karɓar Naira miliyan 10 (dala 100,000), da aka sace daga ma’aikatar lafiya. An gurfanar da tsohuwar ministar lafiya ( Farfesa Adenike Grange ) da mataimakinta da laifin satar sama da Naira miliyan 30,000 (dalar Amurka 300,000) daga cikin kuɗaɗen da ma’aikatar ta ke kashewa tun shekara guda da ta gabata.[8]

A ranar 6 ga watan Yunin 2008 ne aka rantsar da Cif (Mrs) Farida Mzamber Waziri a matsayin sabuwar shugabar hukumar ta EFCC.[1] Sai kuma a ranar 6 ga watan Agusta 2008, tsohon shugaban hukumar Nuhu Ribadu ya samu muƙamin mataimakin sufeto Janar (AIG) zuwa mataimakin kwamishinan ƴan sanda (DCP).[9]

A ranar 14 ga watan Satumba, 2010, an kashe shugaban sashen binciken laifuka na EFCC, Abdullahi Muazu a Kaduna. Ya kasance mai himma wajen yin gwajin shugabannin bankuna da dama.[10]

Shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya sallami Waziri a ranar 23 ga Nuwamba 2011 sannan ya maye gurbin Ibrahim Lamorde a matsayin mukaddashin shugaban wanda majalisar dattawan Najeriya ta tabbatar da shi a ranar 15 ga watan Fabrairu shekara ta 2012.[11]

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya kori Ibrahim Lamorde ne a ranar 9 ga watan Nuwamba, 2015, sannan ya maye gurbinsa da Ibrahim Magu. Majalisar dattawan Najeriya ta ƙi amincewa da tabbatar da Magu a matsayin shugaban hukumar har sau biyu saboda rahotannin tsaro da jami’an tsaron ƙasar suka bayar a ƙasar.[12]

A ranar 6 ga Yuli, 2020, jami’an ma’aikatar harkokin gwamnati da na ƴan sandan Najeriya sun kama Magu, suka kai shi fadar shugaban ƙasa, inda ake so ya amsa wasu tambayoyi game da zargin almundahanar da ake yi masa.[13][14] An tsare shi ne da daddare, kuma a ranar 7 ga watan Yuli aka dakatar da shi daga muƙaminsa na shugaban hukumar har sai an kammala bincike.

A ranar 10 ga watan Yuli, 2020, Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya amince da dakatar da Ibrahim Magu nan take a matsayin shugaban riƙo na Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC)[15] a wata sanarwa da ofishin babban mai shigar da ƙara na ƙasa Abubakar Malami ya fitar. Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kuma amince da cewa daraktan ayyuka na hukumar EFCC Mohammed Umar Abba ya ɗauki nauyin gudanar da ayyukan hukumar[16][17] har sai an kammala bincike da kuma ƙarin umarni. A ranar 16 ga watan Fabrairu, 2021 Shugaba Muhammadu Buhari ya naɗa Abdulrasheed Bawa a matsayin shugaban hukumar ta EFCC.[18][19]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 1.2 "The Establishment Act". Economic and Financial Crimes Commission. 2008. Archived from the original on 2008-01-30. Retrieved 2007-05-17.
  2. Kenton, Will. "Financial Action Task Force (FATF)". Investopedia (in Turanci). Retrieved 2020-05-30.
  3. 3.0 3.1 "Discussion", Engineering for climatic change, Thomas Telford Publishing, pp. 15–16, January 1993, retrieved 2022-12-30
  4. "Head Office Archived 2011-04-11 at the Wayback Machine." Economic and Financial Crimes Commission. Retrieved on 25 July 2011. "Head Office No5 Fomella Street, Off Adetokunbo Ademola Crescent Wuse II Abuja."
  5. "Nigeria arrests runaway governor". BBC. 9 December 2005. Archived from the original on 21 October 2007. Retrieved 2007-05-17.
  6. "Nigeria governors in graft probe". BBC. 28 September 2006. Retrieved 2007-05-17.
  7. "Court declares deportation of Vaswani brothers illegal". Vanguard News. November 4, 2009.
  8. "Minister of Health, Professor Adenike Grange faces corruption probe | Sahara Reporters". saharareporters.com. Retrieved 2023-01-02.
  9. "NUHU RIBADU: IS YARÁDUA LEADING A GOVERNMENT OR A GANG?". Nigeria World. 8 August 2008. Retrieved 2008-09-17.
  10. "Gunmen kill EFCC's forensic team leader in Kaduna". NEXT. 15 September 2010. Archived from the original on 18 September 2010. Retrieved 2010-10-04.
  11. "Waziri's Sack And The Future Of EFCC". P.M. News. November 28, 2011. Retrieved 2011-12-22.
  12. "Again, Senate rejects Magu as EFCC Chairman | Premium Times Nigeria" (in Turanci). 2017-03-15. Retrieved 2022-02-03.
  13. "Answers to five big questions about Magu arrest and probe". BBC News Pidgin. Retrieved 2022-02-03.
  14. "How EFCC's Magu was arrested" (in Turanci). 2020-07-06. Retrieved 2022-02-03.
  15. "Buhari Affirms Magu's Suspension, Directs Mohammed Umar To Take Charge". Channels Television. Retrieved 2022-02-03.
  16. "EFCC picks Director of Operations, Umar to oversee commission". Vanguard News (in Turanci). 2020-07-08. Retrieved 2022-02-03.
  17. "Umar replaces Magu as EFCC chairman". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2020-07-09. Retrieved 2022-05-25.
  18. Adesomoju, Ade (16 February 2021). "Abdulrasheed Bawa to make history as EFCC chairman". premiumtimesng.cm. Retrieved 29 November 2021.
  19. "Cross-examination of EFCC chairman stalled in alleged N761m subsidy fraud". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2021-11-01. Archived from the original on 2022-05-25. Retrieved 2022-05-25.

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]

Labarai[gyara sashe | gyara masomin]