Jump to content

Mustapha Badamasi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Mustapha Badamasi Naburaska

Mustapha badamasi Wanda akafi sani da na buraska ko nabraska dan wasan kwaikwayo ne musamman fannin barkwanci a Masana'antar Kannywood. An haifi Mustapha ashekarar alif dari tara da tamanin da hudu (1984) a Jihar Kano, Najeriya. Ana kiransa da wannan laƙabine sakamakon zuwansa kasar Amurka inda ya samo lambar yabo a wani gari me suna braskem, sannan yayi fim me suna Naburaska.[1][2]

Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Mustapha ya gudanar da rayuwarsane a inda aka haifeshi jihar Kano, mahaifinsa malami shikuma Almajiri ne, anan yayi karatun shi na zamani da addini, yana da aure domin yana da mata biyu da yara shida.

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Yayi karatun addini da na boko tundaga firamare da sakandare a jihar Kano, Arewacin Najeriya sannan yazo Zariya domin cigaba da makarantar gaba da sakandare inda ya fara karatun jami'a a jami'ar Ahmadu Bello dake Zariya.

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Mustapha dan kasuwa ne, dan fim ne, dan siyasa ne. Yafara sana'ar fim/wasan kwaikwayo a shekarar 2001 amma bai shahara ba sai a shekarar 2017, a cikin fim din jarumi nan Adam A Zango mai suna babban yaro Wanda darakta Falalu Dorayi ya bada umarni.

Mukami a gomnatin jihar Kano[gyara sashe | gyara masomin]

A watan Janairun shekarar 2022 mai girma gomnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya nada Mustapha Naburaska a matsayin mai bashi shawara akan labaran farfaganda.[3]

Finafinain jarumin[gyara sashe | gyara masomin]

Jarumin yayi fina-finai da dama amma wadanda suka shahara sune kamar haka:

  1. wankan sikari
  2. babban yaro
  3. dan gaske
  4. basaja da sauran su.

Sannan yana cikin wani fim mai dogon zango a tashar Arewa24 mai suna gidan badamasi.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Daga Bakin Mai Ita tare da Mustapha Naburaska". BBC Hausa. 15 July 2021. Retrieved 12 October 2022.
  2. Lere, Mohammed (15 May 2015). "Tag: Mustapha Naburaska". Premiumtimesng.com. Retrieved 12 October 2022.
  3. Khalid, A'isha (30 January 2022). "Ganduje ya gwangwaje jarumi Naburaska da mukami a gwamnatinsa". Legit.hausa.ng.com. Retrieved 12 October 2022.