Rikicin Kashmir

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Rikicin Jammu da Kashmir (Indiyanci: कश्मीर विवाद, Urdu: مسئلہ کشمیر‎) takaddama ce ta yanki a tsakanin kasashen Indiya da Pakistan. Indiya tana ayyana dukkan yankin da nata ne. A yanzu kuma tana da iko da kashi 43% na yankin, wanda ya hada da yankin Kashmir, Ladakh da kuma Siachen Glacier. Yayinda itakuma kasar Pakistan take da iko da kaso 45% na yankunan Jammu da Kashmir, wanda suka hada da yankunan Azad ta Kashmir da kuma yankunan arewacin Gilgit da Baltistan. Pakistan tace yakamata yayi zaben raba gardama a Kashmir domin tabbatar da samun ra'ayin jama'ar yankin akan kodai ya kasance a Pakistan ko Indiya ko kuma yasamu gashin kan sa.[1] [2]


Infotaula d'esdevenimentRikicin Kashmir

Map
 34°02′00″N 74°40′00″E / 34.0333°N 74.6667°E / 34.0333; 74.6667
Iri yaƙi de Kashmir
Suna saboda Kashmir
Bangare na Indo-Pakistani wars and conflicts (en) Fassara
Kwanan watan 1947
Wuri Kashmir, Jammu da Kashmir
Ƙasa Indiya da Pakistan
Participant (en) Fassara
Adadin waɗanda suka rasu 47,000
Has part(s) (en) Fassara
Indo-Pakistani war of 1947–1948 (en) Fassara
Kargil War (en) Fassara
insurgency in Jammu and Kashmir (en) Fassara
Siachen conflict (en) Fassara
2014 India–Pakistan border skirmishes (en) Fassara
2016–2018 India–Pakistan border skirmishes (en) Fassara
2016 Kashmir unrest (en) Fassara
Indo-Pakistani War of 1965 (en) Fassara

Tarihin rikicin Kashmir[gyara sashe | gyara masomin]

Rikicin ya fara ne lokacin da ake neman bangarewar kasar Indiya a (1947-47). A watan Oktoba 20, 1947, kabilu daban daban suka kokanta da mamayar da kasar Pakistan ke yi a yankunan Kashmir. Da farko dai Maharaja na Jammu da Kashmir ya fara yakar hakan amma ranar 27 ga Oktoba yayi korafi ga babban gwamna na mulkin mallaka wato Louis Mountbatten. Wanda ya amince da hakan, bayan an saka hannu a kan takardun tallafawa Indiya wajen korar sojojin Pakistan ne sai sojojin Indiya suka shiga yankunan na Jammu da Kashmir da umarnin cewa a dakatar da kowanne irin ayyuka na Pakistan a yankunan. Haka kuma Indiya ta kai al'amarin ga Majalisar Dinkin Duniya. Kuma dai ita Majalisar Dinkin Duniyar ta yi kira ga Pakistan data gaggauta da barin yankunan amma kuma ita Pakistan din taki amincewa. A 1947-8 Indiya da Pakistan suka yi yaki karon farko a tsakanin su akan Jammu da Kashmir.

Ruwa[gyara sashe | gyara masomin]

Wani karin dalilin da ya kawo rikicin na Jammu da Kashmir kuma shine Ruwa. Mafiya yawancin kogunan yankunan suna farawa ne daga Kashmir. Wasu daga cikin suna suna haduwa ne a babbar madatsa ta Kogin Indus, kamar su kogunan Jhelum da Chenab. Sune suke wucewa su shiga kasar Pakistan kuma mutane nayin amfani da shi wajen noman rani. Sauran kogunan kamar na Ravi, kogin Beas da na Sutlej suna shiga zuwa arewacin Indiya.

Wani kari daga dalilin haddasuwar rikicin shine Iyaka a 1947, Indiya ce ke iko da mafiya yawancin filayen noman ranin mutanen Pakistan. Kuma kasar ta Pakistan tana fargabar watarana Indiya kan dates hanyoyin ruwan da suka faro daga yankunan da Indiya ke da iko a Kashmir. Wannan kuma kan cutar da tattalin arzikin Pakistan. Anyi yarjejeniya ta ruwan Indus wadda aka sama hannu a 1960 domin daidaita rabon Ruwa.[BBC HAUSA, Rikicin Kashmir 1]

Halin yanzu[gyara sashe | gyara masomin]

Yansanda da masu zanga zanga na fuskantar juna a Kashmir watan Disamba 2018

A yau Kashmir ta kasu kamar haka:

Jamhuriyyar Indiya na iko da yankin Jammu da Kashmir. Wanda ya hada da yankunan Jammu, Kashmir da Ladakh. Pakistan na daukar hakan da yankin da Indiya ke da iko a Kashmir. Yankunan Arewacin Azad Jammu da Kashmir Pakistan ce ke tafiyar da ikon su. Islamabad na kiran su da yankunan Kashmir wanda Pakistan ke da iko. Indiya kuwa na kiran su da yankunan Kashmir da Pakistan ta mamaye.

Yankin da ake kira Aksai Chin kuma kasar Sin ce keda iko da shi. Sannan kuma Sin din tana da iko da yankunan da ta karba daga hannun Pakistan, suna kiran su da Karokoram.[3]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://m.dw.com/ha/tarihin-rikicin-indiya-da-pakistan/av-40377988
  2. https://www.nationalgeographic.com/culture/2019/03/kashmir-conflict-how-did-it-start/
  3. https://hausa.libertytvradio.com/rikicin-kashmir-an-cigaba-da-musayar-wuta-a-tsakanin-indiya-da-pakistan/


Cite error: <ref> tags exist for a group named "BBC HAUSA, Rikicin Kashmir", but no corresponding <references group="BBC HAUSA, Rikicin Kashmir"/> tag was found