Abdulazeez Ibrahim

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abdulazeez Ibrahim
Ɗan Adam
Bayanai
Bangare na Nigerian senators of the 4th National Assembly (en) Fassara da Nigerian senators of the 5th National Assembly (en) Fassara
Jinsi namiji
Ƙasar asali Najeriya
Sunan asali Abdulazeez Ibrahim
Suna Abdelaziz
Sunan dangi Ibrahim
Shekarun haihuwa 27 Nuwamba, 1957
Wurin haihuwa Taraba state
Lokacin mutuwa 5 Oktoba 2021
Yaren haihuwa Hausa
Harsuna Turanci, Hausa da Pidgin na Najeriya
Sana'a ɗan siyasa
Muƙamin da ya riƙe mamba a majalisar dattijai ta Najeriya
Ilimi a Jami'ar Ahmadu Bello
Ɗan bangaren siyasa Peoples Democratic Party
Ƙabila Hausawa

Abdulazeez Abubakar Ibrahim (27 Nuwamba 1957[1] – 5 Oktoba 2021)[2] an zaɓe shi ɗan majalisar dattawa mai wakiltar Taraba ta tsakiya a jihar Taraba, Najeriya a farkon jamhuriya ta huɗu ta Najeriya, yana takara a ƙarƙashin jam'iyyar People's Democratic Party (PDP). Ya hau mulki a ranar 29 ga Mayun shekarar 1999.[3] An sake zaɓen shi a cikin Afrilun shekarar 2003.[4]

Fage[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Ibrahim a shekarar 1957. Ya yi digirin digirgir a fannin Injiniya da harkokin kasuwanci a Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zariya.[5]

Sana'ar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan ya hau kujerarsa a Majalisar Dattawa a watan Yunin shekarata 1999 an naɗa shi kwamitocin kasuwanci (mataimakin shugaban ƙasa), masana'antu, sufurin jiragen sama, Kimiyya da Fasaha, Wutar Lantarki da Ƙarfe, Tsarin Ƙasa da Ayyuka na Musamman.[6] A watan Afrilun 2005 yana cikin wasu Sanatoci da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa da sauran Laifuka (ICPC) ta yi wa tambayoyi game da badaƙalar da aka ce Ministan Ilimi Fabian Osuji ya biya Naira miliyan 55 na cin hanci da rashawa don haka za su yi wa ƙasafin kuɗin ma’aikatar zagon-kasa.[7] A zaɓen da aka yi a watan Afrilun 2007 ya kasance ɗan takarar gwamnan jihar Taraba da ya tsaya takara a jam'iyyar All Nigeria People's Party (ANPP).[8] Ɗanbaba Suntai na PDP ne ya lashe zaɓen.[9]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]