Bolaji Abdullahi
Bolaji Abdullahi | |||
---|---|---|---|
2011 - 2015 ← Akinlabi Olasunkanmi | |||
Rayuwa | |||
Haihuwa | 1969 (54/55 shekaru) | ||
ƙasa | Najeriya | ||
Harshen uwa | Yarbanci | ||
Karatu | |||
Makaranta | Jami'ar Lagos | ||
Harsuna |
Turanci Yarbanci | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa da ɗan jarida | ||
Imani | |||
Jam'iyar siyasa | All Progressives Congress |
Bolaji Abdullahi (an haife shi a shekara ta 1969) ɗan siyasan Nijeriya ne kuma Marubuci daga Jihar Kwara . Ya yi aiki a majalisar ministocin tsohon Shugaban kasan Najeriya, Goodluck Jonathan a matsayin mai Girma Ministan Ci gaban Matasa a watan Yulin 2011 sannan daga baya ya zama Ministan Wasanni. Shine marubucin littafin "Sweet Sixteen" wanda JAMB / UTME 2019-2020 ya karba; Da Kuma littafin sa mai suna "Gold-How Jonathan won and lost Nigeria".
Farkon Rayuwa da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]
Abdullahi ya kammala digiri da mataki na biyu a fannin ilimin yaɗa labarai daga jami'ar Jihar Lagos a 2001.
Ayyuka[gyara sashe | gyara masomin]
A shekarar 1997, Abdullahi ya shiga aikin Jaridar ThisDay a matsayin mai kawo rahoto amma ya bar shekara guda zuwa Taron Shugabancin Afirka. Ya sake dawowa a 2002 inda ya zama Mataimakin Editan Jarida a 2003. Daga baya an nada shi a matsayin Mataimakin na Musamman, Sadarwa da Dabaru ga Gwamnan Jihar Kwara na lokacin, Dokta Bukola Saraki a 2003 sannan daga baya ya zama Mashawarci na Musamman kan Manufofi da Dabaru a 2005. Sannan an nada shi a matsayin Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Kwara daga 2007 zuwa 2011. Ya ci gaba da aiki a majalisar ministocin tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan lokacin da aka nada shi a matsayin Mai Girma Ministan Ci gaban Matasa a watan Yulin 2011 sannan daga baya ya zama Ministan Wasanni.
A watan Disambar 2016, an sanar da Abdullahi a matsayin Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC . A ranar 1 ga watan Agusta, 2018, a hukumance Abdullahi ya sauka daga mukamin sa na Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar All Progressives Congress ya kuma fice daga jam’iyyar.