Damaturu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Globe icon.svgDamaturu

Wuri
Locator Map Damaturu-Nigeria.png Map
 11°45′N 11°58′E / 11.75°N 11.97°E / 11.75; 11.97
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaJihar Yobe
Babban birnin
Labarin ƙasa
Yawan fili 2,366 km²
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci

Damaturu karamar hukuma ce kuma babban birnin jihar Yobe dake arewa maso gabashin Najeriya. Nan ne hedikwata inda fadar gwamnatin Jihar Yobe take wadda gwamna Mai Mala Buni ke mulkinta a halin yanzu, sannan kuma cibiyar gudanar da mulki na jahar. Masarautar Damaturu, ita ce masarautar gargajiya daya jal ta sarkin yanka mai daraja ta daya a gabadaya fadin birnin. Kebantacciyar lambar akwatin waya na birnin ita ce 620. Karamar hukumar tana da fadin kasa 2,366 2 da yawan jama'a 88,014 a ƙidayar 2006. Garin Damaturu yana kan babbar hanyar A3. A alkaluman ilimin zanen kasa, birnin Damaturu ya gindayu ne akan alkaluman kwa'odineto 12°00′00″N 12°00′00″E / 12.00000°N 12.00000°E / 12.00000; 12.00000.

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

Damaturu ta kasance a matsayin mallaka a lokacin da turawan Ingila suka sassaka ta daga gundumar Alagarno . Hakan ya haifar da mamaye daular Bornu a shekara ta 1902 da sojojin mulkin mallaka karkashin jagorancin Kanar Thomas Morland suka yi.

Boko Haram[gyara sashe | gyara masomin]

Damaturu dai ya sha fuskantar hare-haren mayakan jihadi na Boko Haram a yakin da suke yi na kafa daular halifanci a yankin arewa maso gabas.

  • A watan Nuwamba 2011, sun kashe sama da mutane 100 a wasu hare-hare .
  • A watan Disambar 2011, sun kai hare-haren bama-bamai biyu .
  • A watan Yunin 2012, mahara 40 sun shiga gidan yari . Fursunoni 40 ne suka tsere sannan aka kashe mutane takwas.
  • A watan Yunin shekarar 2013 ne mahara suka kai hari wata makaranta inda suka kashe mutane goma sha uku da suka hada da dalibai da malamai.
  • A watan Oktoban shekarar 2013, mayakan sun yi artabu da jami’an tsaro tsawon lokaci tare da kai farmaki a wani asibiti.
  • A watan Disambar 2014, mayakan sun sake kai hare-hare. An ji karar harbe-harbe da fashe-fashe, an kuma ce an kona sansanin 'yan sandan kwantar da tarzoma. Jami'ar jihar Yobe ma an kai hari.
  • A watan Fabrairun 2015, wata matashiya 'yar kunar bakin wake ta kashe mutane 16 a wata tashar mota .
  • A watan Fabrairun 2020, an yi kisan kiyashi a Auno da ke kan babbar hanyar Damaturu zuwa Maiduguri . Maharan sun kashe matafiya 30, sun kona motoci tare da yin garkuwa da mutane.

Yanayi[gyara sashe | gyara masomin]

Nassoshi[gyara sashe | gyara masomin]

11°44′40″N 11°57′40″E / 11.74444°N 11.96111°E / 11.74444; 11.96111Page Module:Coordinates/styles.css has no content.11°44′40″N 11°57′40″E / 11.74444°N 11.96111°E / 11.74444; 11.96111Template:Yobe State