Fatima bint Mundhir

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Fatima bint Mundhir
Rayuwa
Haihuwa 7 century
Sana'a
Sana'a muhaddith (en) Fassara da Islamicist (en) Fassara

Fatima bint al-Munzir bn al-Zubayr ( Larabci: فاطمة بنت المنذر بن الزبير‎ ) (668-763) malamar hadisi ce daga madina, wanda ta kasance daga zuriyar tabi'un .

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Fatima bint Mundhir ta sami iliminta akan hadisai daga Asma bint Abubakar da Ummu Salamah .A matsayin hujjar isar da ilimi daga gare su a cikin jerin masu watsawa a cikin tarin hadisai shida, sunan Fatima bint Mundhir ta mamaye matsayi na biyu.

Gudunmawa ga manyan tarin hadisai shida[gyara sashe | gyara masomin]

hadisai guda 21 a cikin sahihul Bukhari da aka ambaci sunanta,a cikin biyu kai tsaye:a hadisi na 922,a cikin littafi na 11,da hadisi na 5783,a cikin littafi na 76.[1]

A cikin Sahihu Muslim akwai hadisai guda 9,inda a hadisi na 5740 a cikin littafin 39 Fatima bint Muhdhir ta zo tare da diyarta Urwa bint Zubair.[2]

A cikin littafin Sunan Abu Dawud akwai hadisai 5,a cikin Jami'at-Tirmizi akwai hadisai 3, adadinsu daya a cikin Sunnan al-Sughra, a Sunan Ibn Majah kuma hadisai 4 ne.

Gado[gyara sashe | gyara masomin]

Fatima bint Mundhir ta auri dan uwanta Hisham bn Urwah bn al-Zubayr,wanda ya kasance mashahurin malami a hadisai kuma ya haddace hadisai da dama daga wajen antinsa Aisha.[3] Wani abin sha'awa shi ne,ta haddace mafi yawan hadisai fiye da mijinta, saboda koyi da Asmau bint Abubakar. Duk da kasancewarta malamar hadisi,ta zama daya daga cikin manya-manyan wakilan mata na tsararrakin tabi'un,ta samu matsayin faqihi (fakihu).

Nassoshi[gyara sashe | gyara masomin]

  1. http://qaalarasulallah.com/hadith[permanent dead link].
  2. http://qaalarasulallah.com/hadith[permanent dead link].
  3. Waddy, C. (1980). Women in Muslim History. Longmann: University of Virginia, p.72.