Igwe Aja-Nwachukwu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Igwe Aja-Nwachukwu
Ɗan Adam
Bayanai
Jinsi namiji
Ƙasar asali Najeriya
Shekarun haihuwa 31 ga Maris, 1952
Lokacin mutuwa 17 Nuwamba, 2015
Sana'a ɗan siyasa
Muƙamin da ya riƙe Minister of Education of Nigeria (en) Fassara da Minister of Education of Nigeria (en) Fassara
Ilimi a Jami'ar Ibadan

Igwe Aja-Nwachuku (ranar 31 ga watan Maris ɗin 1952 - ranar 17 ga watan Nuwamban 2015) ɗan siyasar Najeriya ne. Ya ƙare wa'adinsa na ministan ilimi a Najeriya a ranar 17 ga watan Disamban 2008. An naɗa shi ministan ilimi watanni goma sha takwas kafin nan.[1][2] Dr. Sam Egwu ya maye gurbinsa a matsayin ministan ilimi. Dokta Aja-Nwachukwu ya kammala karatunsa na digiri na biyu a Jami’ar Ibadan da digirin digirgir (B.Sc) a fannin ƙididdiga, ya yi MBA Finance, M.Sc Statistics da Ph.D a fannin tattalin arziƙi. Sannan yana da Difloma a fannin Kimiyyar Kwamfuta da Injiniya.

Ya fara aikin gwamnati ne a matsayin jami’in ilimi a ma’aikatar ilimi ta jihar Ebonyi a cikin shekarar 1979 a matsayin malamin lissafi. A tsakanin shekarar 1984 zuwa 2006, ya koyar da harkokin kuɗi da kasuwanci a matsayin malami a jami'ar jihar Abia da jami'ar jihar Ebonyi, Abakaliki . Dr. Aja-Nwachukwu ya kuma tsaya takarar gwamnan jihar Ebonyi ta Najeriya a zaɓen shekarar 2007. Ya kasance ɗan Aja Nwachukwu, Ministan Ilimi na Najeriya na farko.

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Jerin mutanen jihar Ebonyi

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. This Day (April 13, 2008). "Nigeria; Aja-Nwachukwu's Delicate Burden". Africa News.
  2. Vanguard (January 2, 2008). "Nigeria; Aja-Nwachukwu's Reforms And 2008 Education Budget". Africa News.