Sam Egwu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Sam Egwu
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

ga Yuni, 2019 -
District: Ebonyi North
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

29 Mayu 2015 -
District: Ebonyi North
Minister of Education of Nigeria (en) Fassara

17 Disamba 2008 - 17 ga Maris, 2010
Igwe Aja-Nwachukwu - Ruqayyah Ahmed Rufa'i
Governor of Ebonyi State (en) Fassara

29 Mayu 1999 - 29 Mayu 2007
Simeon Oduoye - Martin Elechi
Rayuwa
Haihuwa 20 ga Yuni, 1954 (69 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Tarihin Mutanen Ibo
Harshen uwa Harshen Ibo
Karatu
Makaranta Jami'ar Najeriya, Nsukka
Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Enugu
Harsuna Turanci
Harshen Ibo
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Sam Ominyi Egwu CON (an haife shi a ranar 20 ga watan Yunin shekara ta,1954) ɗan siyasar Najeriya ne kuma memba a jam'iyyar People's Democratic Party (PDP) dke Najeriya. An zaɓe shi gwamnan jihar Ebonyi a zaɓen gwamnan jihar Ebonyi a cikin shekarar 1999 daga ranar 29 ga watan Mayun shekarar, 1999 zuwa 29 ga watan Mayun shekara ta, 2007.[1] Dr Egwu an san shi a matsayin ginshiƙi na ci gaban ilimi a jihar Ebonyi da Najeriya.[2] Ya halarci Jami'ar Najeriya, Nsukka inda ya sami digiri na farko a fannin aikin gona a cikin shekarar, 1981. Daga nan ya samu digirin digirgir a fannin aikin gona daga jami’ar Najeriya dake Nsukka a cikin shekarar 1987 da kuma digiri na uku a fannin aikin gona daga jami’ar fasaha ta jihar Enugu a cikin shekarar 1996. Ya kasance babban malami a jami’ar fasaha ta jihar Enugu kuma ya taɓa zama kwamishinan ilimi a jihar Ebonyi ya ba da gudunmawa wajen nasarorin da aka samu a fannin ilimi a lokacin da yake gwamna.[3]

A cikin shekarar 2008, Shugaba Umaru Ƴar'adua ya naɗa shi Ministan Ilimi, inda ya riƙe har zuwa watan Afrilun shekara ta, 2010 lokacin da Farfesa Ruqayyah Ahmed Rufa'i ya maye gurbinsa.[4]

Egwu shine zaɓin tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya zama shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa a babban taronta na ƙasa a cikin shekarar 2008. Duk da haka, a taron da aka yi a ranar 8 ga watan Maris a shekara ta, 2008, ya janye goyon bayan ɗan takara Prince Vincent Ogbulafor, wanda aka zaɓa a matsayin madadin Egwu da babban abokin takararsa, Anyim Pius Anyim.[5]

Zamansa na ministan ilimi ya kasance da ƙungiyar ASUU (Academic Staff Union of Universities) da sauran yajin aikin da ƙungiyoyin jami'o'i ke yi. Hakan ya sa mutane suka nemi a kore shi daga aiki.[6]

A cikin shekarar 2015, ya samu nasarar tsayawa takarar Sanata mai wakiltar Ebonyi ta Arewa a ƙarƙashin jam’iyyar People’s Democratic Party.[7] A halin yanzu, shi ne shugaban kwamitin majalisar dattawa kan masana’antu.[8][9]

Kyaututtuka da karramawa[gyara sashe | gyara masomin]

  • Kwamandan oda na Niger (CON).
  • D.Sc. (Honoriscausa) na Jami'ar Najeriya, Nsukka, 2006.
  • D.Sc. (Honoriscausa) na Ebonyi State University, Abakaliki, 2008.

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Jerin Gwamnonin Jihar Ebonyi
  • Jerin mutanen jihar Ebonyi

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://sunnewsonline.com/2023-ebonyi-governorship-and-zoning-controversy/
  2. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-03-19. Retrieved 2023-03-18.
  3. http://www.gospelhitsnaija.com/promote-your-gospel-song/
  4. https://allafrica.com/stories/201004070116.html
  5. https://allafrica.com/stories/200803090001.html
  6. https://www.vanguardngr.com/2009/07/leave-sam-egwu-alone/
  7. https://www.nigerianeye.com/2015/04/know-your-senators-list-of-senators.html?m=1
  8. https://www.nasco.net/courtesy-visit-by-senate-committee-on-industries/
  9. http://www.aitonline.tv/post-senate_committee_sees_to_procurement_of_locally_made_vehicles