Umar II
![]() | |||||
---|---|---|---|---|---|
24 Satumba 717 - 5 ga Faburairu, 720 ← Sulayman ibn Abd al-Malik (en) ![]() ![]()
706 - 712 ← Hisham ibn Isma'il al-Makhzumi (en) ![]() ![]() | |||||
Rayuwa | |||||
Haihuwa | Madinah, 2 Nuwamba, 681 | ||||
ƙasa |
Umayyad Caliphate (en) ![]() | ||||
Mutuwa |
Church of Saint Simeon Stylites (en) ![]() | ||||
Yanayin mutuwa |
Sababi na ainihi (poisoning (en) ![]() | ||||
Ƴan uwa | |||||
Mahaifi | Abd al-Aziz ibn Marwan | ||||
Mahaifiya | Umm Asim Layla bint Asim | ||||
Yara |
view
| ||||
Yare |
Umayyad dynasty (en) ![]() | ||||
Karatu | |||||
Harsuna | Larabci | ||||
Ɗalibai |
view
| ||||
Sana'a | |||||
Sana'a | ɗan siyasa | ||||
Imani | |||||
Addini | Musulunci |
Umar bn Abdil-Aziz ( Larabci: عمر بن عبد العزيز, romanized: ʿUmar ibn ʿAbd al-ʿAzīz ; 2 Nuwamba 680 – c. 5 February 720 ), wanda aka fi sani da Umar II ( عمر الثاني ), shi ne halifan Umayyawa na takwas . Ya bayar da gagarumar gudunmawa da gyara ga al’umma, kuma an bayyana shi a matsayin “Mafi tsoron Allah da ibada” a cikin sarakunan Banu Umayyawa kuma ana kiransa da Mujaddadi na farko kuma khalifan Musulunci na shida. [1]
Ya kuma kasance dan uwa ga tsohon halifan, kasancewarsa dan kanin Abdul-Malik, Abd al-Aziz . Ya kuma kasance jikan halifa na biyu, Umar ibn Al-Khattab .
An kewaye shi da manyan malamai, an ba shi umarni da ya tattara hadisai na farko a hukumance da kwadaitar da ilimi ga kowa da kowa. Ya kuma aika da jakadu zuwa kasashen Sin da Tibet inda ya gayyaci sarakunansu da su karbi Musulunci . sannan kuma ya kasance yana da hakuri da ‘yan kasa wadanda ba musulmi ba. A cewar Nazeer Ahmed, a zamanin Umar bn Abdil-Aziz ne addinin Musulunci ya samo asali kuma ya samu karbuwa a wajen dimbin al'ummar Farisa da Masar .
Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]
- ↑ Hoyland, In God's Path, 2015: p.199