Aisha Pamela Sadauki
1986 - Disamba 1987 ← Dabid Mark - Lawan Gwadabe → | |||
| Rayuwa | |||
| Haihuwa | Zaria, 12 ga Afirilu, 1949 (77 shekaru) | ||
| ƙasa | Najeriya | ||
| Karatu | |||
| Makaranta |
Jami'ar Ahmadu Bello Jami'ar Tsaron Nijeriya | ||
| Harsuna |
Turanci Hausa Pidgin na Najeriya | ||
| Sana'a | |||
| Sana'a | ɗan siyasa da minista | ||
Aisha Pamela Sadauki 'yar siyasa ce a Najeriya wacce ta kasance kwamishina kuma mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna a lokacin mulkin soja na Abubakar Tanko Ayuba.[1]
Tarihi
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Pamela Sadauki a shekarar 1945. Ta halarci makarantar mishan ta Katolika na St-Louis da ke Kano kuma ta sami digiri na farko a fannin Home Economics tare da digiri na biyu a fannin Nutrition daga Jami'ar Jihar Iowa a shekarar 1968.[2] An naɗa ta mataimakiyar gwamnan Jihar Kaduna a watan Agusta na shekarar 1990 a lokacin mulkin soja na Janar Ibrahim Babangida.[3] Sannan daga baya an naɗa ta Kwamishina a Jihar Kaduna, Ci gaban Al'umma, Matasa da Wasanni a shekarar 1988, Kwamishina a Ilimi a shekarar 1989 da Mataimakiyar Gwamnan Kaduna daga shekarar 1990 zuwa 1992.
Rayuwa ta sirri
[gyara sashe | gyara masomin]Aisha Pamela Sadauki ta auri tsohon ministan Najeriya David Ahmed Sadauki wanda ya rasu a shekara ta 2008.[4]
Kyaututtuka
[gyara sashe | gyara masomin]Ƙungiyar Manoman Dabbobi ta Najeriya ta ba ta lambar yabo ta Medal of Honor a shekarar 1999. Ta sami lambar yabo ta National Honorary Medal of Officer of the Order of Nigeria (OON) a shekarar 2000.