Haliru Dantoro

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Sarki kuma ɗan Siyasar Najeriya
Ɗan Adam
Bayanai
Jinsi namiji
Ƙasar asali Najeriya
Shekarun haihuwa 1938
Wurin haihuwa New Bussa
Lokacin mutuwa 30 Oktoba 2015
Sana'a ɗan siyasa
Muƙamin da ya riƙe mamba a majalisar dattijai ta Najeriya da ma'aikatar Babban birnin tarayya

Haliru Dantoro Kitoro III (1938 – ranar 30 ga watan Oktoban 2015) basaraken gargajiya ne kuma ɗan siyasa a Najeriya. A ranar 26 ga watan Fabrairun 2002 ya zama Sarkin Masarautar Borgu, Jihar Neja ta gargajiya ce, a ranar 26 ga watan Fabrairun 2002, bayan hamɓarar da magabacinsa, Alhaji Isiaku Musa Jikantoro.[1] Ya yi sarauta har zuwa rasuwarsa a ranar 30 ga watan Oktoban 2015.[1]

Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Dantoro a cikin shekarar 1938, ɗan ƙarami a cikin yara uku da iyayensa suka haifa,[2] garinsu shine New Bussa. Ya yi aiki a gwamnatocin mulkin soja na jihar Kwara a lokacin gwamnatin Yakubu Gowon. Dantoro ya riƙe muƙamin kwamishinan noma na tsawon shekara ɗaya da rabi kuma ya riƙe muƙamin kwamishinan kuɗi na tsawon watanni shida, sannan aka naɗa shi kwamishinan kasuwanci har zuwa juyin mulkin shekarar 1975 a ranar 29 ga watan Yuli wanda ya kawo sabuwar gwamnati. Gwamnati ta gaba ta naɗa shi shugaban hukumar The Herald, jaridar da jihar ke ɗaukar nauyinsa. A cikin shekarar 1976, an naɗa Dantoro a matsayin shugaban hukumar kula da kogin Neja, ƙungiyar da ke taimakawa manoma a jihohin Kwara, Neja da Kaduna.

A jamhuriya ta biyu, ya kasance mataimakin shugaban jam’iyyar NPN na jihar Kwara, ya kuma yi ministan babban birnin tarayya a takaice a cikin shekara ta 1983 a lokacin gwamnatin shugaba Shehu Shagari.[2] Sai dai ba zato ba tsammani, juyin mulkin Najeriya ya kawo ƙarshen naɗinsa na Ministan Babban Birnin Tarayya a cikin watan Disamban 1983.[2]

Dantoro ya kuma yi aiki a matsayin Sanata a cikin shekara ta 1992 a matsayin memba na National Republican Convention, tsohuwar jam'iyyar siyasa.[1]

Sarki Haliru Dantoro ya rasu ne a wani asibiti a ƙasar Jamus bayan gajeruwar rashin lafiya a ranar 30 ga watan Oktoban 2015, yana da shekaru 77 a duniya.[1]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 1.2 1.3 https://www.premiumtimesng.com/news/more-news/192419-emir-of-borgu-haliru-dantoro-kitoro-iii-is-dead.html?tztc=1
  2. 2.0 2.1 2.2 "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2018-04-02. Retrieved 2023-04-08.