Jump to content

Harin Bam a Jos, 2014

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentHarin Bam a Jos, 2014
Map
 9°56′N 8°53′E / 9.93°N 8.88°E / 9.93; 8.88
Iri aukuwa
car bombing (en) Fassara
Kwanan watan 20 Mayu 2014
Wuri Jos
Ƙasa Najeriya
Adadin waɗanda suka rasu 118
Adadin waɗanda suka samu raunuka 56

A ranar 20 ga watan Mayun shekara ta 2014, wasu bama-bamai biyu sun tashi a birnin Jos na jihar Filato a Najeriya, inda suka kashe mutane aƙalla 118 tare da jikkata wasu fiye da 56.[1] Bam na farko ya tashi ne a wata kasuwa, na biyu kuma kusa da wata tashar mota. Ko da yake babu wata ƙungiya ko wani mutum da ya ɗauki alhakin kai hare-haren, ana danganta hare-haren da ƙungiyar Boko Haram,[2] wacce tayi ƙaurin suna na kai hara hare da dama a Najeriya, musamman yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Kiristoci da Musulmai sun yi arangama da dama a birnin Jos acikin shekaru da dama kafin tashin bama-bamai, kuma ƙungiyar ta Boko Haram ma ta yi ta kai ruwa rana kafin harin.[1] A shekarar 2012, ƙungiyar Boko Haram ta kai wa wasu majami'u hari da bama-bamai da nufin assasa rikicin addini tsakanin Kirista da Musulmi.[1] A cikin watan da ya gabato harin Boko Haram, na sace 'yan matan makaranta sama da 200, [1] ko da yake birnin Jos ya fuskanci manyan hare-hare guda biyu tun daga shekara ta 2012.[1] Kwana ɗaya bayan tashin bama-baman an kashe mutane 27 a hare-haren wasu kauyuka.[2]

Fashewar bama-baman kwara biyu sun kasance mintuna 30 tsakani,[1] ɗaya ya fashe da karfe 3:00, ɗayan kuma da ƙarfe 3:30.[3] Fashewar farko ta faru ne a Kasuwar Terminus, inda aka samu asarar rayuka sama da hamsin.[4] A cikin Terminus akwai "asibitin koyarwa, shaguna, ofisoshi da kasuwa" kafin harin. [5] Na biyu ya faru ne a kusa da wani asibiti. [4] Kuma ya kashe masu aikin ceto, waɗanda suka je taimakawa bayan tashin bam na farko. [1] An kuma ga yadda hayaki mai yawa ya turnike wurin. [4] Mai yiyuwa ne an shirya tashin bama-baman ne domin yin sanadin asarar rayuka da dama.[1] Bam ɗin da aka ɗana a cikin motar ya sa motocin da ke kusa da wurin suka tarwatse.[5]

Jami’an kashe gobara da masu aikin ceto sun yi ƙoƙarin isa wuraren da bama-baman suka tashi, amma “dubban” mutane ne ke tserewa daga yankin.[1] An sanya bama-baman don kashe mutane da yawa, ba tare da nuna bambanci ba na addini [1] ta hanyar amfani da dabara, (ta kashe mutane, bayan anzo ana ceton waɗanda suka jikkata, sai kuma a tashi bam na biyu da zai yi sanadiyar mutuwar Mutanen wurin ciki hard waɗanda suka je bada agajin gaggawa).[3][1] Sojoji sun kafa shingayen binciken ababen hawa a yankin, inda wasu suka gudanar da binciken ababen hawa. Ana sa ran adadin gawarwaki zai ƙari, [5] kuma an ƙona wasu gawarwakin da ba a iya tantance su ba.[3] Adaɗin waɗanda suka mutu ya kai 46 cikin sauri zuwa adadi na 118 yayin da aka share baraguzan ginin wuraren da suka ruguje.[3] Duk da haka, wasu sun ƙiyasta adadin ya kai 150.[6]

Gida Najeriya

[gyara sashe | gyara masomin]
  •  Nigeria – Shugaba Goodluck Jonathan ya yi Allah-wadai da tashin bama-baman,[1] ya kuma kira harin da "mummunan hari kan ƴancin ɗan adam",[1] su kuma mayaƙan ya kira su da, "masu zalunci da mugunta".[3]

Ƙasashen Duniya

[gyara sashe | gyara masomin]
  •  Turkey Ma'aikatar Harkokin Waje (Turkiyya) ta bayyana cewa, "Mun samu labari da bakin ciki game da waɗannan hare-haren bama-bamai". Turkiyya ta yi kakkausar suka ga hare-haren da ake kai wa ‘yan Najeriya, tare da mika ta’aziyyarmu ga gwamnatin Najeriya da al’ummarta da kuma fatan samun sauki ga waɗanda suka jikkata.[7]
  •  United Kingdom – Sakataren harkokin wajen Birtaniya, William Hague ya kira harin da aka kai a Jos a matsayin "laifi mai ban tsoro da rashin mutuntaka".[2]
  •  United States Ma'aikatar Jiha ta Amurka ta baƙin mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurkan, ta ce harin bam, da sauran hare-haren baya-bayan nan da aka ɗora wa alhakinsa kan ƙungiyar Boko Haram, ayyukan ta’addanci ne marasa kan gado.[2]
  1. 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 "Nigerian twin bomb explosions kill dozens in Jos". BBC. 20 May 2014. Retrieved 20 May 2014.
  2. 1 2 3 4 "Nigeria violence: 'Boko Haram' kill 27 in village attacks". BBC. BBC. 21 May 2014. Retrieved 21 May 2014.
  3. 1 2 3 4 5 Jonah, Adamu; Igboeroteonwu, Anamesere (20 May 2014). "Bombings kill at least 118 in Nigerian city of Jos". Reuters. Retrieved 21 May 2014.
  4. 1 2 3 "2 explosions hit bus station in central Nigeria city". Fox News. 20 May 2014. Retrieved 20 May 2014.
  5. 1 2 3 Mark, Monica (21 May 2014). "Nigeria bombings leave over a hundred dead in city of Jos". The Guardian. Retrieved 21 May 2014.
  6. "none". The Punch Nigeria Vol 38, No 20, 666. 21 May 2014. pp. 1, 2 & 7. Missing or empty |url= (help)
  7. "Turkey condemns Nigerian bombings". TurkishPress.com. 21 May 2014. Archived from the original on 22 May 2014. Retrieved 22 May 2014.