Harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentHarin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna
Iri aukuwa
mass shooting (en) Fassara
Garkuwa da Mutane
Kwanan watan 28 ga Maris, 2022
Wuri Jihar Kaduna
Nufi Nigerian Railway Corporation
Adadin waɗanda suka rasu 60
Perpetrator (en) Fassara Ƴan ƙungiyar fashi a Najeriya
Makami improvised explosive device (en) Fassara
Bindiga

A ranar 28 ga Maris, 2022, an kai hari kan wani jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna a Katari, jihar Kaduna, Najeriya. A martanin da ta mayar, hukumar kula da layin dogo ta Najeriya (NRC) ta dakatar da ayyukan hanyar na ɗan takaitaccen lokaci.[1][2]

Lamarin[gyara sashe | gyara masomin]

Da misalin ƙarfe 7:45 na dare, an yi garkuwa da ɗaruruwan fasinjojin da ke tafiya arewa kan hanyarsu ta zuwa yankin arewa maso yammacin Najeriya a Katari,[3] jihar Kaduna, yayin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan jirgin Abuja zuwa Kaduna, suka kashe tare da jikkata wasu.[4]

Kimanin fasinjoji 970 ne ke cikin jirgin,[5] kuma mai yiwuwa ƴan fashin sun yi awon gaba da wasu da dama cikin daji da wasu 'yan fashi da suka iso kan babura riƙe da bindigogi da wasu muggan makamai,[6][7] a cewar wani fasinja da ya tsere daga harin.[8]

Jirgin ya taso daga tashar Idu da ke Abuja da karfe 6 na yamma kuma an shirya ya isa tashar jirgin Rigasa ta Kaduna da ƙarfe 8 na dare[9][10] Kamar yadda shaidun gani da ido suka tabbatar, an kai wa jirgin ruwan bama-bamai sau biyu kafin ƴan bindigar ɗauke da makamai su buɗe wuta kan fasinjojin dake cikin jirgin.[11] Duk da cewa an ba da sanarwar ɓacewar fasinjoji 26 a hukumance, ya zuwa ranar 4 ga Afrilu, sama da fasinjoji 150, ba a san inda suke ba.[12][13][14]

Kashe-kashe[gyara sashe | gyara masomin]

Sama da mutane sittin (60) ne, aka kashe da suka haɗa da: Amin Mahmoud, shugaban matasa na jam'iyyar All Progressives Congress, APC, Chinelo Megafu Chinelo, likita, Tibile Mosugu, lauya mai tasowa kuma dan babban lauyan Najeriya, Barista Musa Lawal- Ozigi, sakatare-janar, Trade Union Congress, TUC.[15][16]

Wata likita mai suna Megafu Chinelo ta rasu ne sa’o’i bayan ta bayyana a shafinta na Twitter cewa an harbe ta ne a cikin jirgin ƙasa da ke kan hanyarsa ta zuwa Kaduna.[17] A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 28 ga Maris, 2022, ƙungiyar likitocin Najeriya (NMA) ta tabbatar da hakan.[18][19] Chinelo ya wallafa a shafinsa na Twitter jim kaɗan bayan harin da ƴan ta’adda suka kai wa jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna inda ya ce: “Ina cikin jirgin, an harbe ni. Don Allah a yi mini addu’a.”[20]

Hare-hare na baya-bayan nan[gyara sashe | gyara masomin]

Lamarin ya faru ne a cikin rikicin ‘yan bindigan Najeriya kwanaki biyu bayan wani farmaki da ƴan bindiga suka kai a filin jirgin sama na Kaduna, inda aka kashe jami’an hukumar kula da sararin samaniyar Najeriya (NAMA) biyu tare da yin garkuwa da wasu ma’aikata da dama.[21] A cikin Oktoba 2021, NRC ta dakatar da ayyukan kan hanyar a karon farko saboda wannan dalili.[22][23]

Bayan haka[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan harin, sojojin saman Najeriya sun kai samame a dajin da ke kan iyakar jihar Neja da jihar Kaduna, inda suka kashe ‘yan ta’adda ƙasa da su 34, kamar yadda jaridar The Guardian ta ruwaito.[24]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Suspected bandits attack Nigerian passenger train". Reuters. 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  2. "Gunmen attack Kaduna-bound train in Northern Nigeria". 28 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  3. "Rail staff killed in 'unprecedented' attack on train in Nigeria". TheGuardian.com. 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  4. "Loud blast, gunshots as suspected bandits attack Nigerian train". Reuters. 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  5. "About 900 passengers feared kidnapped as bandits bomb Abuja-Kaduna train". 28 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  6. "Abuja-Kaduna train: How bandits attack interstate train wey carry more dan 900 passengers". BBC News Pidgin. 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  7. "Many Feared Killed, Others Kidnapped As Bandits Attack Abuja-Kaduna Train". Channels Television. 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  8. "Suspected bandits attack passenger train in northern Nigeria". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  9. "Again bandits attack train station in Kaduna". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  10. "BREAKING Bandits Bomb Kaduna Train Station With Explosive Devices Hours After Train Bombing". 29 March 2022. Archived from the original on 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  11. Nimi Princewill (April 1, 2022). "Gunshots everywhere': Survivor of train ambushed by armed gang in Nigeria reveals harrowing details". Cable News Network. Retrieved April 5, 2022.
  12. "More Than 150 Still Missing After Kaduna Train Attack". Channels Television.
  13. Elian Peltier; Ben Ezeamalu (March 30, 2022). "A Safe Route No More: Nigerians Mourn Victims of Deadly Train Attack". New York Times. Retrieved April 5, 2022.
  14. Abubakar Ahmadu Maishanu (April 4, 2022). "One week after Kaduna train attack, 168 passengers still unaccounted for – NRC". Premium Times. Retrieved April 5, 2022.
  15. "Kaduna-Abuja train bomb NMA reacts to killing of Dr Chinelo, makes demands from Buhari govt". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  16. "Abuja-Kaduna Train Attack: Politician, medical doctor, unionist among dead passengers". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  17. "Abuja-Kaduna Train Attack: Doctor Confirmed Dead, Hours After Calling For Prayers". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  18. "NMA mourns medical doctor, Chinelo, who died in Kaduna train attack". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  19. "NMA mourns female doctor killed in Kaduna train attacks". 30 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  20. "Grief, anger over death of young Nigerian doctor in Abuja-Kaduna train attack". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  21. "Nigeria: Train attack leaves several dead". Deutsche Welle. 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  22. "Halting bandits' threat to all modes of transport in Kaduna". 30 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  23. "Nigeria Railway Corporation confirms attack on Abuja-Kaduna train". 29 March 2022. Retrieved 23 February 2022.
  24. "Aftermath of Kaduna train bombing: Military raids kill scores of terrorists". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2022-04-01. Retrieved 2022-04-02.