Mohammed Umar Bago
|
|
Wannan mukalar bata da Reference (Manazarta) ko daya, ka taimaka ta hanyar samar da Manazarta daga littafi ko yanar gizo, duba wannan shafin domin samun masaniya akan yanda zaka samar da Reference (Manazarta) a cikin wannan mukalar.
|
2023 -
11 ga Yuni, 2019 - District: Chanchaga
6 ga Yuni, 2015 - | |||||||
| Rayuwa | |||||||
| Haihuwa | Minna, 22 ga Faburairu, 1974 (51 shekaru) | ||||||
| ƙasa | Najeriya | ||||||
| Ƴan uwa | |||||||
| Abokiyar zama |
Hajiya Fatima Umaru Bago (en) | ||||||
| Karatu | |||||||
| Makaranta |
Jami'ar, Jos Jami'ar Ambrose Alli Jami'ar Usmanu Danfodiyo Jami'ar Calabar | ||||||
| Harsuna |
Turanci Hausa Pidgin na Najeriya | ||||||
| Sana'a | |||||||
| Sana'a | ɗan siyasa da Ma'aikacin banki | ||||||
| Imani | |||||||
| Addini | Musulunci | ||||||
| Jam'iyar siyasa |
Action Congress of Nigeria All Progressives Congress | ||||||
Mohammed Umar Bago an haife shi a ranar 22 ga watan Fabrairu shekara ta alif 1974, a garin Minna da ke jihar Niger a Najeriya, Kuma cikakken Banufe ne, dan siyasa a Najeriya. Shi ne danmajalisan mai wakiltan yankin Chanchaga a majalisan taraiyyan Najeriya. Ya nimi kujeran kakakin majalisan taraiyan Najeriya, Kuma ya samu sakamako na biyu yayin da Femi Gbajabiamila ya lashe zaben a shekara ta dubu biyu da shatara (2019). Sannan kuma cikakken dan jam'iyar All Progressive Congress wato (APC).
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]Rayuwar farko da Ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]An haife shi a shekara ta alif 1974, Hon. Umar Bago ya halarci Makarantar Firamare ta Marafa, Minna da Kwalejin Gwamnatin Tarayya dake Jos. Ya sami takardar shaidar karatu ta yammacin Afirka WAEC. Ya sami digiri na farko a kimiyyar siyasa a Jami'ar Usman Danfodio, Sokoto.
Hon. Umaru Bago ya sami mabanbanta diflomar bayan da digiri dakuma digiri na biyu, gami da difloma na digiri na biyu a kan fannin gudanarwa daga Jami'ar Fasaha ta Tarayya Minna a shekara ta 2001, Master of Business Administration (MBA) a gudanar da sha'anin kasuwanci a Jami'ar Ambrose Ali, Ekpoma, a shekara ta 2003, da kuma digiri na biyu a fannin kudi a Jami'ar Calabar a shekara ta 2005. Ya kuma kasance fitaccen tsohon ɗalibi ne daga Jami'ar Cambridge a Ingila a shekarar 2014. [1]
- ↑ Obi, Ifoh (11 June 2019). "Gbajabiamila Beats Bago To Emerge Speaker 9th Assembly". Newsreel Daily (in Turanci). Archived from the original on 8 July 2020. Retrieved 8 July 2020.