Rasheed Ladoja

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Rasheed Ladoja
Gwamnan jahar oyo

7 Disamba 2006 - 28 Mayu 2007
Adebayo Alao-Akala - Adebayo Alao-Akala
Gwamnan jahar oyo

29 Mayu 2003 - 12 ga Janairu, 2006
Lam Adesina - Adebayo Alao-Akala
Rayuwa
Cikakken suna Rashidi Adewolu Ladoja
Haihuwa 25 Satumba 1944 (79 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Yarbawa
Harshen uwa Yarbanci
Karatu
Makaranta University of Liège (en) Fassara
Harsuna Turanci
Yarbanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Rashidi Adewolu Ladoja (an haife shi 25 ga watan Satumba a shekara ta 1944) ɗan kasuwa ne wanda ya zama gwamnan jihar Oyo a Najeriya a ranar 29 ga watan Mayu a shekara ta 2003 a matsayin ɗan jam'iyyar PDP. An tsige shi a watan Janairun a shekara ta 2006, amma a watan Disambar a shekara ta 2006 aka dawo da shi bakin aiki. Wa’adinsa ya kare a shekarar 2007. Ladoja ya zama memba na Zenith Labour Party (ZLP) a cikin watan Disamba a shekara ta 2018.[1]

Rayuwar farko[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Ladoja a ranar 25 ga watan Satumba a shekara ta 1944 a kauyen Gambari kusa da Ibadan . Ya halarci makarantar sakandare ta maza ta Ibadan a shekara ta (1958 zuwa shekara ta 1963) da makarantar Olivet Baptist High School a shekara ta (1964 zuwa shekara ta 1965). Ya yi karatu a Jami'ar Liège, Belgium a shekara ta (1966 zuwa shekara ta 1972) inda ya sami digiri a fannin Injiniya. Ya samu aiki a kamfanin mai na Total Nigeria, inda ya yi aiki na tsawon shekaru 13 a mukamai daban-daban kafin ya shiga kasuwanci na zaman kansa a shekarar 1985. Abubuwan da ya shafi kasuwancinsa sun hada da sufuri, masana'antu, banki, noma da sufuri. An zabe shi a majalisar dattawan Najeriya a shekarar 1993 a lokacin jamhuriya ta uku ta Najeriya a kankanin lokaci, ya kasance memba a jam'iyyar United Nigeria Congress Party (UNCP) a lokacin mulkin Abacha. A shekara ta 2000, Ladoja ya zama darakta na bankin Standard Trust Limited. [2]

Gwamnan jihar Oyo[gyara sashe | gyara masomin]

An zabi Ladoja a matsayin gwamnan jihar Oyo a watan Afrilun a shekara ta 2003 a tutar XDAjam’iyyar PDP, kuma ya karbi mulki a ranar 29 ga watan Mayu a shekara ta 2003. Ya samu goyon bayan Alhaji Lamidi Adedibu, masu fada aji na PDP a jihar oyo. A watan Agustan shekarar 2004, Ladoja da Adedibu sun shiga tsaka mai wuya game da rabon wadanda gwamnati ta nada. Ladoja bai samu goyon bayan jam’iyyar ba a wannan rigimar. A wata hira da aka yi da shi a karshen shekarar 2005, shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ahmadu Ali, ya ce Ladoja ya kamata ya karbi umarni daga Lamidi Adedibu.

A ranar 12 ga watan Janairun Shekara ta 2006 ne ‘yan majalisar dokokin jihar Oyo suka tsige Ladoja tare da tilasta musu barin aiki. An rantsar da mataimakinsa, Christopher Adebayo Alao-Akala a matsayin sabon gwamna. A ranar 1 ga watan Nuwamba, a shekara ta 2006, Kotun Daukaka Kara da ke babban birnin jihar, Ibadan, ta bayyana tsigewar ba bisa ka'ida ba, amma ta ba da shawarar jiran tabbatar da wannan hukunci daga Kotun Koli. Kotun koli ta amince da hukuncin a ranar 11 ga watan Nuwamba, a shekara ta 2009, kuma Ladajo ya koma ofishin a hukumance a ranar 12 ga watan Disamba shekara ta 2006. An girke jami’an ‘yan sandan kwantar da tarzoma a kan manyan titunan manyan ofisoshin gwamnati domin dakile tashin hankalin magoya bayan Adebayo Alao-Akala da Lamidi Adedibu a lokacin da aka mayar da shi bakin aiki. [3]

Ladoja ya kasa lashe zaben fitar da gwani na PDP a matsayin dan takara karo na biyu. Ya zabi ya goyi bayan ‘yan takarar Action Congress na zaben shugabannin kananan hukumomi 33. PDP ta ki shiga zaben. Hakan ya sa jam'iyyar Action Congress (AC) ta lashe kujeru 26 sannan jam'iyyar ANPP ta lashe kujeru bakwai. Sai dai magajinsa a matsayin gwamna, tsohon mataimakinsa kuma tsohon mukaddashin gwamna Christopher Adebayo Akala, ya kori shugabannin kansilolin jim kadan da hawansa mulki tare da maye gurbinsu da magoya bayan PDP.

Bayan ajeye aiki[gyara sashe | gyara masomin]

A ranar 28 ga watan Agusta a shekara ta 2008, Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta kama Ladoja bisa zargin rashin fitar da kudaden da aka sayar da hannun jarin gwamnati da ya kai N1.9. biliyan a lokacin gwamnatinsa. Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta tsare shi na dan wani lokaci a gidan yari a ranar 30 ga watan Agusta a shekara ta 2008. An bayar da belinsa ne a ranar 5 ga watan Satumba a kan kudi naira miliyan 100 tare da masu tsaya masa guda biyu kan kudi daya. A watan Maris na shekarar 2009, wani tsohon mataimaki ya ba da shaida kan yadda aka raba kudaden rabon tsakanin iyalan Ladoja, mai gadin sa, manyan ‘yan siyasa da lauyoyi.

Ladoja ya kasance dan takarar gwamna a jam’iyyar Accord a jihar Oyo a zaben watan Afrilun shekara 2011 da kuma shekara ta 2015, ya sha kaye a hannun Sanata Abiola Ajimobi . Daga baya ya koma jam’iyyarsa ta Accord Party zuwa PDP a shekarar 2017. Rigimar PDP ta sanya shi da sauran abokansa (daga Labour Party, All Progressives Congress APC da sauransu) suka koma Jam'iyyar A

African Democratic Congress (ADC) a shekara ta 2018. Bayan ɗan gajeren zaman da aka yi a ADC wanda ya tabbathaduwarsu waje dayan gado, Ladoja tare da mabiyansa sun koma Zenith Labour Party (ZLP) a cikin Disamba a shekara ta 2018.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2022-06-29. Retrieved 2022-06-29.
  2. https://tribuneonlineng.com/we-are-ready-to-welcome-ladoja-back-to-accord-party-%E2%80%95-national-secretary/
  3. https://www.thisdaylive.com/index.php/2022/01/07/ladoja-uninformed-people-responsible-for-tension-over-olubadan-stool/