Sani Musa Danja
![]() | |
---|---|
![]() | |
Rayuwa | |
Cikakken suna | Sani Musa Abdullahi |
Haihuwa | Fagge, 20 ga Afirilu, 1973 (50 shekaru) |
ƙasa | Najeriya |
Harshen uwa | Hausa |
Karatu | |
Harsuna |
Turanci Hausa Pidgin na Najeriya |
Sana'a | |
Sana'a | Jarumi |
Imani | |
Addini | Musulunci |
Sani Musa Abdullahi, wanda aka fi sani da Sani Danja ko kuma Danja {An haife shi a ranar 20 ga watan Afrilu shekarata alif ɗari tara da saba'in da Uku1973} Miladiyya. jarumin fim ne a Nijeriya, furodusa, darekta, mawaƙi kuma mai rawa. Yana shiga cikin masana'antar Kannywood da Nollywood. A watan Afrilun shekara ta dubu biyu da Sha takwas 2018 ne Etsu Nupe, Yahaya Abubaka suka nada shi a matsayin Zakin Arewa. Ya kasance ɗaya daga cikin shahararrun yan wasan kwaikwayo a Kannywood.
Aiki[gyara sashe | gyara masomin]
Ya shiga harkar finafinan Hausa a shekarar 1999 a amatsayin dalibi. Haka kuma Danja ya shirya kuma ya shirya finafinai, ciki har da Manakisa, Kwarya tabi Kwarya, Jaheed, Nagari, Wasiyya, Harsashi, Gidauniya, Daham, Jarida, Matashiya, da sauransu. Ya fara fitowa a Nollywood a shekara ta 2012 a cikin 'Yar Kogin.
Fina-finai[gyara sashe | gyara masomin]
Sani Musa Danja ya yi, ya shirya kuma ya ba da umarni a fina-finan Kannywood da Nollywood . Daga cikinsu akwai:
Sunan Fim | Shekara |
---|---|
Yar agadez | 2011 |
A Cuci Maza | 2013 |
Albashi (Albashi) | 2002 |
Bani Adam | 2012 |
Budurwa | 2010 |
Da Kai zan Gana | 2013 |
Daga Allah ne '' (Daga Allah ne) | 2015 |
Daham | 2005 |
Dan Magori | 2014 |
Duniyar nan | 2014 |
Fitattu | 2013 |
Gani Gaka | 2012 |
Gwanaye | 2003 |
Hanyar Kano | 2014 |
Kukan Zaki (Kukan zaki) | 2010 |
Daya bangaren | 2016 |
Buri uku a duniya (Buri guda uku a duniya) | 2016 |
Iyali[gyara sashe | gyara masomin]
Sani danja ya auri Mansura Isah yana da yara hudu.