Abubakar Sani Bello
|
| |||||
13 ga Yuni, 2023 - District: Gundumar Sanatan Neja ta Arewa
29 Mayu 2015 - 29 Mayu 2023 ← Mu’azu Babangida Aliyu | |||||
| Rayuwa | |||||
| Cikakken suna | Abubakar Sani Bello | ||||
| Haihuwa | Jihar Neja, 17 Disamba 1967 (58 shekaru) | ||||
| ƙasa | Najeriya | ||||
| Ƴan uwa | |||||
| Abokiyar zama | Amina Abubakar Bello | ||||
| Karatu | |||||
| Makaranta | Jami'ar Maiduguri | ||||
| Matakin karatu |
BSc Economics and Politics (en) | ||||
| Harsuna |
Turanci Hausa Pidgin na Najeriya | ||||
| Sana'a | |||||
| Sana'a | Ma'aikacin banki | ||||
| Imani | |||||
| Jam'iyar siyasa | Action Congress of Nigeria | ||||
Abubakar Sani Bello An haife shine a ranar 17 ga watan Disamban shekara ta alif ɗari tara da sittin da bakwai 1967) Miladiyya.a jihar Neja, Najeriya. Ɗan siyasar Najeriya, wanda shine tsohon Gwamnan Jihar Niger, Nigeria daga ranar 29 ga watan Mayun shekarar 2015 zuwa ranar 29 ga watan Mayun shekarar 2023.[1] Y anzu kuma sanata mai wakiltar Gundumar Sanatan Neja ta Arewa,a Majalisar dattawan Najeriya.
Tasowarsa da karatunsa
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Abubakar Sani Bello a ranar 17 ga watan Disamban shekarar 1967.[2] Ɗan tsohon gwamnan mulkin soja na tsohuwar jihar Kano, Kanar Sani Bello. Ya yi makarantar firamare ta St. Loius da ke Kano daga shekara ta 1974 zuwa 1979 sannan ya tafi Makarantar Soja ta Najeriya daga shekara ta 1980 zuwa shekara ta 1985, Ya yi karatu a Jami'ar Maiduguri daga shekara ta 1986 zuwa 1991, inda ya sami digiri na biyu a fannin tattalin arziƙi. Ya yi aiki a wurare daban-daban a ƙasar nan, tun daga lokacin da ya yi NYSC, inda aka tura shi aiki a Fatakwal a sashen kasuwanci na NICOTES Services a matsayin Supervisor.[3]
Aikin siyasa
[gyara sashe | gyara masomin]Neman gwamna:
Alhaji Abubakar Sani Bello ya lashe zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Neja, APC a zaɓen 2015. Ya samu ƙuri'u’u 3,829 inda ya doke Sanata Musa Ibrahim a zaɓen fidda gwani. Daga baya ya ci gaba da lashe babban zaben da jimillar kuri’u 593,709. Hukumar INEC ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen a ranar 13 ga Afrilu, 2015. A ranar 9 ga Maris, 2019, aka sake zaɓen shi a matsayin Gwamnan Jihar Neja.[4][5]
A ranar 24 ga watan Agustan shekara ta 2020, ya amince da kwamitin sulhu da sauran kwamitoci a wani taron kwamitin zartarwa na Jiha, tare da ‘yan majalisar dokoki ta kasa daga jihar ƙarƙashin jagorancin Sanata Aliyu Sabi Abdullahi da sauran shugabannin jam’iyyar. Manufar wannan kwamiti ita ce sake ginawa da kuma sake fasalin jam’iyyar domin samun kyakkyawan aiki a zaɓukan 2023.[6][7]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2018-06-14. Retrieved 2018-12-19.
- ↑ "Abubakar Sani-Bello Archives". Vanguard News (in Turanci). Retrieved 2023-06-17.
- ↑ "Abubakar Sani Bello". Politicians Data (in Turanci). 2018-05-22. Retrieved 2023-06-17.
- ↑ https://www.premiumtimesng.com/regional/north-central/319328-gov-bello-of-niger-secures-second-term-wins-in-all-25-lgs.html
- ↑ "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-06-13. Retrieved 2023-12-29.
- ↑ https://www.thisdaylive.com/index.php/2020/08/02/x-raying-five-years-of-sani-bellos-niger/
- ↑ https://dailypost.ng/2020/05/25/ipac-rates-niger-state-gov-abubakar-sani-high-on-rule-of-law/