Adil al-Kalbani

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Adil al-Kalbani
Rayuwa
Haihuwa Riyadh, 3 ga Afirilu, 1959 (65 shekaru)
ƙasa Saudi Arebiya
Harshen uwa Larabci
Karatu
Makaranta King Saud University (en) Fassara
Harsuna Larabci
Sana'a
Sana'a Liman
Imani
Addini Mabiya Sunnah

Adil al-Kalbani ( Larabci: عادل الكلباني‎ ) Malamin addinin Musulunci ne ɗan asalin ƙasar Saudiyya, wanda ya kasance limamin babban masallacin Makkah.[1][2][3]

Tarihin rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Adil al-Kalbani a birnin Riyadh a ranar 4 ga watan Afrilu, shekara ta 1958 gidan su sun kasance talakawa kuma waɗanda sukayo hijira daga Ras Al Khaimah na Hadaddiyar Daular Larabawa wadanda suka zo Saudiyya a shekarun 1950. Saboda halin babu da Ahalinsa suke ciki, al-Kalbani ya samu aiki da kamfanin jirgin saman Saudi bayan ya kammala makarantar sakandare, a lokacin kuma fara halartar darussan yamma a Jami'ar Sarki Saud.

Malamin farko da Al-Kalbani ya fara yi a karatuttukansa na Musulunci shi ne Hasan bn Gaanim al-Gaanim. Ya karanci Sahihul Bukhari da Jami` at-Tirmidhi da tafsirin Ibn Kathir a wurinsa. Ya kuma yi karatu a wurin Mustafa Muslim wanda ya koyar da tafsirin al-Baydawi a jami'ar Musulunci ta Imam Muhammad ibn Saud. Sannan ya karanci Akhir Tadmariyah wajen Abdullahi Ibn Jibrin, sannan ya karanci Alqur'ani wurin Ahmad Mustafa. A shekarar 1994 ya ci jarrabawar gwamnati na zama Liman.

Fara Limancin sa[gyara sashe | gyara masomin]

Ya taba yin mafarki cewa ya zama limami a Babban Masallacin Makka; Bayan shekaru biyu, a shekara ta 2008, Sarki Abdullahi ya zaɓe shi don jagorantar sallar tarawihi a masallaci.

A birnin Bandu na ƙasar Japan, Al-Kalbani ya ziyarci cibiyar Minhaj-ul-Qur'an a ranar 30 ga watan Yuni, 2013.

Al-Kalbani ya ce shi ba Shaihi ba ne (Mai bada da'awa a Addinin Musulunci) amma Qari ne.

Rayuwar Sirrin[gyara sashe | gyara masomin]

Yana da mata biyu da ƴaƴa goma sha biyu.

Ra'ayin sa[gyara sashe | gyara masomin]

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na twitter, al-Kalbani ya bayyana cewa rashin kasancewar ƙararrawar coci a kasar Saudiyya ya faranta masa rai.

Faɗuwar Injin ɗaukar a Makka[gyara sashe | gyara masomin]

Al-Kalbani ya soki wani sakon da wani mawakin Saudiyya ya wallafa a shafinsa na Twitter inda ya ce Injinan da ya faɗo a Makkq "sun faɗo ƙasa a inda ake Sallah". Al-Kalbani ya ce, wannan shi ne irin wauta mafi muni. Cikin ba'a ya ba da shawarar cewa sauran injinan ba su rushe ba saboda suna da "Kyau sosai".

Al-Kalbani ya bayyana cewa Salafiyya ita ce tushen akidar ISIL.

Rabawa tsakanin Maza da Mata[gyara sashe | gyara masomin]

Ya soki yadda ake raba tsakanin Mata da Maza a masallatai, inda mata suke keɓewa can wani gefe daban inda Maza basa Iya ganin suma kuma basa ganin mazan. Sai dai suje muryar Liman a Ansakuwwa (Lasifika). Ya kira wannan da "Nuna ƙyama ga mata" ("phobia of women")

Ƴan Shi'a[gyara sashe | gyara masomin]

Cikin wata hira da BBC, al-Kalbani ya ayyana Shi'a goma sha biyu a matsayin masu ridda, wanda ya haifar da martani daga mabiya dariƙar Sunnah ta Saudiyya. A shekara ta 2019, sai ya janye matsayinsa bayan ya karanta wani littafi na wani ɗan’uwansa malami Hatim al-Awni, inda ya bayyana cewa, ya daina kallon waɗanda suka yi ridda a matsayin waɗanda suka “yi imani da Allah ɗaya, suna cin naman mu [halal], kuma suna yin sujada zuwa ga alƙibla.

Matsayinsa gameda kayan kaɗe-kaɗe[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin fatawar, al-Kalbani ya ɗauki waƙa a matsayin halaltacciya a shari’ar Musulunci, sai dai daga baya ya janye wannan fatawar a shekarar 2010. A shekarar 2019 ya sake canza ra'ayinsa game da waƙa inda ya sake bayyana cewa waƙa ba Haram nace a Musulunci. Al-Kalbani ya halarci taron waƙa ta addini. An zargi cewa any amfani da sarewa a lokacin gudanar da wannan waƙar.

Shiga Harkar Fina-finai[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin watan Nuwamba shekarar 2021 ya bayyana a cikin wani bidiyo na talla Combat Field - Riyadh Season 2021.

Shafin yanar gizo na waje[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Worth, Robert F. (April 10, 2009). "A Black Imam Breaks Ground in Mecca". The New York Times. Riyadh.
  2. "Former Mecca Grand Mosque's Imam: Clerics can make mistakes like politicians". Al Arabiya English (in Turanci). 2020-02-12. Retrieved 2020-08-03.
  3. Sheriff, Othman. "The First Black Saudi Imam Heads for Sierra Leone: a Rejoinder". Critique Echo. Retrieved 27 August 2020.