Rann, Borno

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Rann, Borno

Wuri
Map
 12°16′N 14°28′E / 12.27°N 14.46°E / 12.27; 14.46
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaJihar Borno

Rann birni ne da ke a jihar Bornon Najeriya, da ke kusa da kan iyaka da Kamaru. Ya kasance gida ne ga sansanin 'yan gudun hijira.[1][2]

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

Rann yana ɗaya daga cikin yankunan arewa maso gabashin Najeriya da suka zama masu isa ga kungiyoyin agaji. A hankali ana ƙara taimakon agajin gaggawa a wuraren da a baya ba a iya kaiwa gare su. A Rann, kusan mutane 43,000 ne ke gudun hijira a cikin gida kuma suna fama da matsanancin ƙarancin abinci da matsanancin rashin abinci mai gina jiki. Samun kai agaji zuwa yankin na da wahala saboda rashin tsaro da kuma munanan hanyoyi, kamar yadda ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar.[3] A ranar 17 ga watan Janairun shekarar 2017 ne sojojin saman Najeriya suka kai harin bam a sansanin bisa kuskure, laamarin da ya yi sanadiyar muutuwar mutane aƙalla 52 tare da jikkkata sama da 100.[2][4][5]

A ranar 14 ga watan Janairu, 2019, 'ƴa

n Boko Haram sun mamaye garin Rann a yayin da ake ci gaba da samun karuwar hare-haren ta'addanci a yankin,[6] tare da lalata su, da tarwatsa mazauna garin da yawa daga kan iyaka zuwa Bodo na Kamar.[1][7] A lokacin, garin ya kasance gida ga yan gudun hijira 35,000. Ko da yake tun farko an danganta harin da ISWAP na bangaren Abu Musab al-Barnawi, amma daga baya ƙungiyar Boko Haram ta Abubakar Shekau ta ɗauki alhakin kai harin.[7] Duk da haka sojojin Najeriya da kawayen Kamaru sun sake kwace garin Rann, daga baya sun yi watsi da shi, don haka ƙungiyar Boko Haram ta sake kai wani hari a garin a ranar 28 ga watan Janairun 2019. Mayaƙan sun sake cinna wuta a matsugunin, sun kashe dattawan yankin, tare da sa dubun-nan mutane tserewa.[8] A wannan karon, ƴan gudun hijirar daga Rann sun ƙaura zuwa Goura a yankin Arewacin Kamaru.[9]

A watan Agustan 2021, ƴan ta'addan ISWAP, sun mamaye Rann waɗanda suka lalata barikin yankin tare da wawashe matsuguni kafin su koma cikin daji.[10]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 Thomas Joscelyn; Caleb Weiss (17 January 2019). "Thousands flee Islamic State West Africa offensive in northeast Nigeria". Long War Journal. Retrieved 24 February 2019.
  2. 2.0 2.1 Quinn, Ben; Akinwotu, Emmanuel (17 January 2017). "Nigeria air strike: dozens dead as camp for internally displaced people hit by mistake". The Guardian. Retrieved 18 January 2017.
  3. EMERGENCY RESPONSE MOBILISED FOLLOWING AIRSTRIKE ON RANN LOCALITY.
  4. Stephanie Busari and Ibrahim Sawab (January 17, 2019). "Nigerian fighter jet strikes refugees, aid workers in Borno". CNN.
  5. Searcey, Dionne (17 January 2017). "Nigerian Jet Mistakenly Bombs Refugee Camp, Killing Scores". The New York Times. Retrieved 18 January 2017.
  6. "Islamic State insurgents overrun northeast Nigerian town: security..." 14 January 2019. Retrieved 21 January 2019 – via www.Reuters.com.
  7. 7.0 7.1 Fergus Kelly (17 January 2019). "Shekau Boko Haram faction claims attack in Rann, Nigeria". Defense Post. Retrieved 24 February 2019.
  8. Paul Carsten (1 February 2019). "After Nigerian army abandoned town, Boko Haram slaughtered at least 60". Reuters. Retrieved 24 February 2019.
  9. "'No other possibility but to leave': UN News special report from the Nigeria-Cameroon border as 35,000 newly-displaced seek safety". UN News. 1 February 2019. Retrieved 17 August 2018.
  10. Wale Odunsi (1 September 2021). "Borno: ISWAP claims 10 Nigerian troops died in Rann attack". Daily Post. Retrieved 23 September 2021.