Ummarun Dallaje

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ummarun Dallaje
Rayuwa
ƙasa Najeriya
Sana'a
Imani
Addini Musulunci

Sarkin Musulmin katsina mujahidi malam ummarun Dallaje, wakilin sarkin Musulmi na baki daya na usmanu Dan fodio, yayi jihadi a ƙarƙashin tutan mujaddadi usmanu Dan fodio ne a shekarar ta 1807, ya rasu a shekarar 1835, Allah ya jikanshi da rahma amin, shine sarkin Dallazawa na farko.[1] sakamakon jihadin da yayi a jihar Katsina ya fatattaki sarkin katsina Magaji Haladu, yayan shi da jikokin shi sun mulki katsina har zuwa lokacin turawan mulkin mallaka jihar katsina a shekara ta 1903 karkashen jagorancin lord lugard, an tumbuke sarkin katsina Abubakar a shekara ta 1905 aka sa sarki Yaro dan Musa shima aka tumbuke shi aka sa sarki Muhammad Dikko a shekara ta 1906 har zuwa mutuwan shi a shekarar ta 1944 wanda shi basullube ne, Allah ya jikansu duka da rahma amin.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Fari, Abubakar A. (2016-12-30). "Who is who in Katsina?". Daily Trust (in Turanci). Retrieved 2020-10-09.