Waliyi Abdurrahim-Maiduniya

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Waliyi Abdurrahim-Maiduniya, wanda ake kiransa wani lokachin da Sheikh Abdurrahim ibn Ibrahim ibn Shi'ithu ibn Ghali, daga masarautar Kano yake kuma malamin addinin musulunci ne da yayi rayuwa a kasar Kadawa, ta Karamar Hukumar Warawa ta jihar Kano.[1]

Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Waliyi Abdurrahim-Maiduniya ya kuma fito daga dangin Awliya Banu Gha Madinawa Malamai, zuriar Imam Ghali (Malam Gha),[2][3][4][5][6][7][8][9]wasu daga cikin dangin sa sunyi ikirarin asalinsu daga Banu Hashim ne, Gidan Quraishawa wanda Larabawa ne, ta kuma wajen Sharif ibn Ali wanda ahalinsa suke mulkin kasar Morroco kuma wanda suke dangin Annabi Muhammadu ne,[10]ana kiran dangin nasa da sunan Madinawa saboda tarihin da ya nuna daga Madina suke,[11].[12][13][14]

Ya auri mata da dama a ciki har da Maryam Muhammad Inuwa Chango bafulatana daga garin Chango a Karamar hukumar Warawa ta dangin mahaifinta,[15]kuma yar Jobawa Fulani ta hanyar mahaifiyarta.[16]mahaifiyarta Binta yar Sarkin Sumaila Akilu ce wanda ya fito daga tsatson Makaman Kano Iliyasu da Makaman Kano Isa na Daya,[17]wanda suka rike sarautar Hakimichi a kasar Wudil, Garko, Takai da Sumaila Local Governments)[18]

Shi ne Kakan Abdullahi Aliyu Sumaila na wajen uba.[19]

Karamomi[gyara sashe | gyara masomin]

Waliyi Abdurrahim Maiduniya ya kasance Limamin Kasar Kadawa ta Karamar Hukumar Warawa wanda aka itifakin Waliyi ne saboda Karamonin da yayi a zamanin rayuwarsa[20][21]

Tarihi ya nuna yayi zuhudu har wani lokachin ya na yin kwanaki bai ci abinchi ba.[22]A masarautar Kano jama'a suna yin zaton Waliyi ne, Kabarinsa yana Kadawa.[23][24][25]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Auwalu, Ali (2001). Kano Malam Abdu Maiduniya. River Front Press.
  2. Bashir, Ali (2000). Kano Malams in the Ninteenth Century. River Front Press.
  3. Hassan, Mohammed (2018). Islamic Religious Practices and Culture of the Al-Ghali Family. Tafida Printing Press.
  4. Abubakar, Badamasi. Trans Saharan Trade: Networks and Learning in Ninetenth Century Kano. Danjuma Press.
  5. Aminu, Muhammad. The History of Al-Ghali Family. Gargaliya Press.
  6. Sani, Muhammadu (1990). Arab Settlers in Kano. Sauda Voyager.
  7. Balogun, Ismail A.B (1969). The penetration of Islam into Nigeria. Khartoum: University of Khartoum,Sudan, Research Unit.
  8. Danlami, Yusuf (2005). Al-Ghali Family and its Religious Leaders. Danlami Printers.
  9. Tarikh Arab Hadha al-balad el-Musamma Kano. Journal of Royal History. 1908.
  10. Balarabe, Suleman (1987). The History of Kadawa Town. Bala Printing Press.
  11. Abdullahi, Ahmed (1999). Madinawan Kano. Kano: Danlami Printers.
  12. Norris, H.T. (1975). The Tuaregs:Their Islamic Legacy and Its Diffusion in the Sahel. England: Aris and Phillips,Ltd.
  13. Last, Murray (1967). The Sokoto Caliphate. New York: Humanities Press.
  14. Bello, Ahmadu (1962). My Life. Cambridge University Press.
  15. Sumaila, Ahmed Abdullahi (2001). The History of Fulanin Chango. Kano: Kadawa Gaskiya Press.
  16. Salisu, Yakubu (2007). History of Chango Town. Kadawa Gaskiya Press.
  17. Idris Rimi, Abdulhamid (1991). The History of Sumaila. Zaria: Institute of Administration,Ahmadu Bello University.
  18. Aliyu, Sumaila. Jobe, a clan compendium.
  19. Sumaila, Ahmed (2003). The making of a Public Servant: Abdullahi Aliyu Sumaila. Kano: Kadawa Gaskiya Press.
  20. Santali, Muhammadu (1981). The Kadawa Imams. River Front Press.
  21. Abdullahi, Ahmed (2004). Maliki School of thought in the Kano Emirate. River Front Press.
  22. Muhammad, Ahmed (2013). The Zuhudu of Malam Abdu Maiduniya. Kano: Cipsco Printers.
  23. Sumaila, Ahmed (2005). History of Islamic Education in Kano State:The Example of Imam Al-Ghali Zawiya. Kano: Kadawa Gaskiya Press.
  24. Sani, Abdulkadir (2007). Al-Fiqh-Al-Akbar-An-Accurate-Translation. Mandawari Press.
  25. Bashari, Tukur (2014). Madinawa and Their Teachings. Voyager Publications.