Kabiru Gombe

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Kabiru Gombe
Rayuwa
Haihuwa Yamaltu/Deba, 1 ga Yuni, 1969 (54 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Karatu
Harsuna Hausa
Larabci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a Malamin addini
Fafutuka Salafiyya
Imani
Addini Musulunci

Sheik Muhammad Kabiru Haruna GombeTemplate:Audt An haifi Malam a garin Kuri a Karamar Hukumar Yamaltu Deba, da ke a jihar Gombe. Malam ya yi makarantar firamare a garin Gombe, a Islamiyya ta Izala a nan garin Gombe.[1] A nan ne Sheikh Kabiru Gombe ya samu haddar Al-Qur'ani mai girma tare da gyara karatunsa a wajen malamai irin su : Sheikh Zarma Gombe, Da Sheikh Dr. Abdullahi Saleh Pakistan. Ya kuma yi karatunsa na ilimi a wajen maluma irin su Sheikh Usman Isah Taliyawa Gombe. Sheikh Kabiru Gombe ya zama Alaramma mai jan baki a kungiyar Izala tun yana karami, kafin daga bisani ya juya zuwa mai wa'azi wanda a halin yanzu duniyar Hausa take amfana da wa'azinsa. Sheikh Kabiru Gombe bai tsaya iya wa'azi ba, yana taba kasuwanci, sannan babban manomi ne. Malam yana da mata hudu da 'ya'ya da jikoki. Malam yana da baiwa kwarai, domin duk abun da malam ya haddace to da wuya ka ga wannan abu ya salwanta a kwakwalwarsa. Yana daya daga cikin malamai masu kima a cikin al'umma kuma jama'a na son jin karatunsa musamman ma idan aka ce wa'azin kasa ko kuma irin karatu ko nasiha da ya shafi cikin gida (

ma'ana na auratayya).

Farkon rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Da'awa[gyara sashe | gyara masomin]

Zargi[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

Wannan Muƙalar guntuwa ce: tana buƙatar a inganta ta, kuna iya gyara ta.