Kabiru Gombe

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Simpleicons Interface user-outline.svg Kabiru Gombe
Rayuwa
Haihuwa Yamaltu/Deba
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Karatu
Harsuna Hausa
Larabci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a Malamin addini
Fafutuka Salafiyya
Imani
Addini Musulunci

Sheik Muhammad Kabiru Haruna GombeTemplate:Audt An haifi Malam a garin Kuri a Karamar Hukumar Yamaltu Deba, wadda take a jihar Gombe. Malam ya yi makarantar firamare a garin Gombe, a islamiyya ta Izala a nan garin Gombe. A nan ne Sheikh Kabiru Gombe ya samu haddar ALQUR'ANI mai girma tare da gyara karatunsa a wajen malamai irin su : Sheikh Zarma Gombe, Da Sheikh Dr. Abdullahi Saleh Pakistan. Ya kuma yi karatunsa na ilimi a wajen maluma irin su Sheikh Usman Isah Taliyawa Gombe. Sheikh Kabiru Gombe ya zama Alaramma mai jan baki a Kungiyar Izala tun yana karami, kafin daga bisani ya juya zuwa mai wa'azi wanda a halin yanzu duniyar Hausa take amfana da wa'azinsa. Sheikh Kabiru Gombe bai tsaya iya wa'azi ba, yana taba kasuwanci, sannan babban manomi ne. Malam yana da mata hudu da 'ya'ya da jikoki. Malam yana da baiwa kwarai, domin duk abun da malam ya haddace to da wuya ka ga wannan abu ya salwanta a kwakwalwarsa Allah ya kara wa rayuwar Sheikh albarka ameen. Yana daya daga cikin malamai masu kima acikin al'umma kuma jama'a nason jin karatunsa musamman ma idan akace wa'azin kasa ko kuma irin karatu ko nasiha da ya shafi cikin gida ( ma'ana na auratayya).

Farkon rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Da'awa[gyara sashe | gyara masomin]

Zargi[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

Wannan Muƙalar guntuwa ce: tana buƙatar a inganta ta, kuna iya gyara ta.