Saad al Ghamidi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Saad al Ghamidi
Rayuwa
Cikakken suna سعد بن سعيد بن سعد الغامدي
Haihuwa Dammam, 7 ga Augusta, 1967 (56 shekaru)
ƙasa Saudi Arebiya
Harshen uwa Larabci
Karatu
Makaranta Jami'ar Imam Muhammad ibn Saud Islamic
Harsuna Larabci
Sana'a
Sana'a Q109016709 Fassara da Gemara (en) Fassara
Imani
Addini Musulunci

Sa'ad al-Ghāmidī ( Larabci: سعد الغامدي‎; An haife shi a shekarar 1967) mahaddaci ne kuma limamin babban masallaci mai alfarma Masjid an-Nabawi. Al-Ghamdi ya zama limami ga al'ummar musulmi a faɗin duniya.[1]

Tarihin Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi al-Ghāmidi a Dammam, Saudi Arabia a shekara ta 1967. Ya haddace Al-Qur'ani mai girma gaba dayansa a shekarar 1990 lokacin yana ɗan shekara 22. Ya shahara a bangare tajwidi. Ya karanci bangaren shari'ar Musulunci (Islamic Studies) a Dammam, musamman a mazhabar Shari'a, tushen dokokin addinin musulmi . A shekarar 2012 aka nada shi a matsayin Limamin Masallacin Yousef bin Ahmed Kanoo da ke birnin Dammam kafin nan ya jagoranci sallah a masallatai da dama na duniya ciki har da Amurka da Ingila da Ostiriya.

A cikin Ramadan a shekarar 2009, Sheikh Sa'd al-Ghāmidi ya shugabanci sallar Tarāwīḥ a al-Masjid an-Nabawi (Madina's Holy site of Islam) na Madina.

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. News, Arab (28 July 2018). "FaceOf: Sheikh Khalid Al-Ghamdi, Imam at the Grand Mosque in Makkah". Arabnews.com. Arabnews. Retrieved May 22, 2023.

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]