Garba Nadama

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Garba Nadama
gwamnan jihar Sokoto

1982 - Disamba 1983
Shehu Kangiwa - Garba Duba
Rayuwa
Haihuwa 1938
ƙasa Najeriya
Mutuwa 4 Mayu 2020
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Jam'iyyar National Party of Nigeria
Peoples Democratic Party

Garba Nadama (1938 - 4 ga Mayun shekarar 2020) ɗan siyasar Najeriya ne wanda ya kasance gwamnan farar hula na biyu a Jahar Sokoto, Najeriya, a cikin ɗan gajeren lokaci a Jamhuriyyar Najeriya ta Biyu, ya riƙe muƙamin daga Janairun 1982 zuwa Nuwambann shekarar 1983. Ya gaji Shehu Kangiwa, wanda ya rasu a hatsarin Polo.[1]

Tarihin Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Garba Nadama ya samu digirin digirgir (Ph.D). a tarihi daga Jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya a shekarar 1977.[2]

Nadama ya kasance babban abokin hamayyar Alhaji Ibrahim Gusau na jam’iyyar NPN a matsayin mataimakin gwamnan Sokoto a shekarar 1979.[3] An bayyana shi a matsayin mai shiru, ɗan birni kuma ɗan siyasa mai ra'ayin mazan jiya.[4] A watan Yulin 1982 Jihar Sakkwato ta samu rancen Naira miliyan 96 daga Bankin Duniya.[5] A watan Disambar 1982, Gwamnatin Tarayya ta baiwa Jihar Sakkwato Naira 400,000 domin yin amfani da su wajen rage zaizayar guguwa. Nadama ya bayyana adadin a matsayin kaɗan kuma bai isa ya magance matsalar ba.[6] A ranar 8 ga Maris 1993 ya ƙaddamar da sabon na'urar watsa shirye-shirye ga Hukumar Talabijin ta Najeriya dake Gusau.[7] An kafa Federal Polytechnic, ƙaura-Namoda (yanzu a jihar Zamfara) a lokacinsa.[8]

Nadama ya bar mulki ne bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a shekarar 1983 inda Manjo Janar Muhammadu Buhari ya karɓi mulki.[1][9]

Nadama ya zama mamba a majalisar kawo sauyi ta siyasa ta ƙasa, sannan ya kuma zama fitaccen ɗan jam’iyyar PDP.[4] Nadama ya zama darakta na bankin Societe Generale Bank Nigeria (SGBN).[10] A watan Afrilun 2008, ya kasance mataimakin sakataren ƙasa na kwamitin da zai duba shawarwarin warware bambance-bambancen cikin gida a cikin PDP.[11]

Nadama ya mutu ne a ranar 4 ga Mayun 2020 sanadiyyar COVID-19[12] kuma ya bar mata huɗu da ƴaƴaa goma sha takwas.[13][14]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 https://www.worldstatesmen.org/Nigeria_federal_states.htm
  2. https://nigeriaworld.com/articles/2005/nov/151.html
  3. http://allafrica.com/stories/200811100171.html
  4. 4.0 4.1 http://allafrica.com/stories/200901140197.html?page=3
  5. https://apps.dtic.mil/sti/pdfs/ADA352751.pdf
  6. https://apps.dtic.mil/sti/pdfs/ADA364977.pdf
  7. https://apps.dtic.mil/sti/pdfs/ADA363494.pdf
  8. http://fedpolykauran.com/index.htm[permanent dead link]
  9. https://apps.dtic.mil/sti/pdfs/ADA337954.pdf
  10. https://web.archive.org/web/20091222091415/http://www.globip.com/pdf_pages/african-vol4-article5.pdf
  11. http://allafrica.com/stories/200804010222.html
  12. https://theeagleonline.com.ng/former-sokoto-governor-dies-during-protracted-illness-amid-rising-covid-19-cases/
  13. https://punchng.com/former-sokoto-governor-dies-at-82/
  14. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2020-06-28. Retrieved 2023-03-14.