Habu Daura
Habu Daura | |
---|---|
Ɗan Adam | |
Bayanai | |
Jinsi | namiji |
Ƙasar asali | Najeriya |
Yaren haihuwa | Hausa |
Harsuna | Turanci, Harshen Ijaw, Hausa da Pidgin na Najeriya |
Writing language (en) | Turanci |
Sana'a | ɗan siyasa |
Muƙamin da ya riƙe | Gwamnan Jihar Bayelsa |
Ƙabila | Hausawa |
Habu Daura shine kwamishinan ƴan sanda ya kasance shugaban riƙo na jihar Bayelsa dake Najeriya yana riƙe da muƙamin daga cikin watan Fabrairu zuwa Yuni shekara ta 1997 a lokacin mulkin soja na Janar Sani Abacha.[1][2] A cikin shekarar 1999, Nuhu Ribaɗu, wanda a lokacin jami’in shari’a ne a hukumar ƴan sanda ta hukumar leƙen asiri da bincike, ya bayar da shawarar a gurfanar da Daura a gaban kuliya bisa zarginsa da hana gudanar da bincike kan laifukan fashi da makami a shekarar 1999. Daura ya yi ritaya daga aikin ƴan sanda.[3]
Shugaba Umaru Ƴar'adua ya naɗa Daura a matsayin ma'aikacin hukumar ƴan sanda (PSC) a cikin shekarar 2008 a matsayin mamba na dindindin.[3][4] Nuhu Ribaɗu wanda shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya naɗa shugaban hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa, sannan kuma Ƴar’aduwa ya kore shi, ya bayyana Daura a matsayin wanda bai cancanta ba kuma bai dace ba, yana mai nuni da shawarar da ya bayar tun farko a gurfanar da Daura.[5] A kwanakin baya ne dai hukumar ta PSC ta sauke Ribaɗu daga muƙamin mataimakin sufeto-Janar na ƴan sanda zuwa mataimakin kwamishinan ƴan sanda.[6]
Daura ya jagoranci tawagar PSC masu sa ido a zaɓen watan Fabrairun shekara ta 2010 a jihar Anambra. Rahoton nasa ya ce ƴan sandan sun nuna hali mai kyau, amma an cire akwatunan zaɓe a wasu rumfunan zaɓe.[7]
Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]
- ↑ https://web.archive.org/web/20110724143253/http://www.bayelsa.gov.ng/new/index.php?option=com_content&view=article&id=109:bayelsa-state&catid=47:the-state&Itemid=111#
- ↑ https://www.worldstatesmen.org/Nigeria_federal_states.htm
- ↑ 3.0 3.1 https://web.archive.org/web/20100419071249/http://www.noprin.org/policenews.html#
- ↑ https://web.archive.org/web/20100824075407/http://www.psc.gov.ng/node/133
- ↑ https://odili.net/news/source/2008/oct/30/800.html[permanent dead link]
- ↑ https://allafrica.com/stories/200810300953.html
- ↑ https://allafrica.com/stories/201002080616.html