Joyce Msuya

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Joyce Msuya
Rayuwa
Haihuwa Tanzaniya, 1968 (55/56 shekaru)
ƙasa Tanzaniya
Mazauni Nairobi
Mutuwa Dar es Salaam
Karatu
Makaranta University of Strathclyde (en) Fassara
University of Ottawa (en) Fassara
Sana'a
Sana'a microbiologist (en) Fassara da environmental scientist (en) Fassara
Employers Majalisar Ɗinkin Duniya

Joyce Msuya 'yar ƙasar Tanzaniya ce mai nazari a fannin halittu kuma masaniya a fannin kimiyyar muhalli wacce ke aiki a matsayin Mataimakiyar Sakatare-Janar kan Harkokin Jin Daɗin Jama'a da Mataimakiyar Mai Gudanar da Agajin Gaggawa a Ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya mai Kula da Ayyukan Jin kai tun a shekarar 2021. [1] Daga shekarun 2018 zuwa 2021, ta yi aiki a matsayin mataimakiyar Darakta a Hukumar Kula da Muhalli ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNEP) a matakin mataimakiyar Sakatare-Janar.[2]

Rayuwar farko da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Msuya a Tanzaniya, kusan shekarar 1968.[3] Ta sami digiri na farko na Kimiyya a Biochemistry da Immunology daga Jami'ar Strathclyde, Glasgow, Scotland, a shekara ta 1992. Daga baya ta kammala karatun digiri na biyu da digiri na uku a Kimiyyar Halittu da Immunology daga Jami'ar Ottawa, Ontario, Kanada, a shekarar 1996.

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Farkon aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Kafin shiga rukunin Bankin Duniya, Msuya ta yi aiki a matsayin Manazarciyar Manufofin Kiwon Lafiya na Duniya tare da Cibiyar Nazarin Duniya ta Liu (yanzu Cibiyar Liu don Al'amuran Duniya ) a Jami'ar British Columbia a Kanada. A baya, ta yi aiki a Tanzaniya a kan ayyuka daban-daban, na masu zaman kansu da na gwamnati.[4]

Aiki a Bankin Duniya[gyara sashe | gyara masomin]

Msuya ta shiga bankin duniya a shekarar 1998 a matsayin ƙwararriya a fannin lafiya. Ta ci gaba da haɓaka ƙwararru a fannin tattalin arziƙin ci gaba tare da ba da lamuni a fannin kiwon lafiya a lokacin da take aiki a bankin duniya na sake ginawa da bunƙasa (International Bank for Reconstruction and Development). A cikin shekarar 2001, ta zama Mataimakiyar Shugaban Ci gaban tattalin arziki na Bankin Duniya a matsayin mai ba da shawara ga Babban Mataimakin Shugaba da Babban Masanin Tattalin Arziƙi, Farfesa Lord Nicholas Stern.[4] Daga shekarun 2005 zuwa 2011, ta yi aiki a International Finance Corporation, a cikin Sashen Dabarun Ayyuka da Manufacturing, Agribusiness & Services, inda ta kai matsayin Babbar Jami'iyyar Dabarun.

A shekarar 2011, an naɗa Msuya a ofishin Cibiyar Bankin Duniya ta Beijing a matsayin mai kula da yankin Gabashin Asiya da tekun Pasifik, inda ta mai da hankali kan tallafawa ayyukan Bankin a kokarinta na "yaki da talauci da inganta wadatar juna". A cikin watan Afrilu 2014, babban jami'in gudanarwa ya zaɓi Msuya don kafawa da sarrafa ofishin rukunin farko na Bankin Duniya a Jamhuriyar Koriya, tayi aiki na tsawon shekaru uku a matsayin Wakiliyar Bankin Duniya na Musamman ga Jamhuriyar Koriya kuma Shugabar Rukunin Bankin Duniya (WBG) Ofishin da ke Songdo, Incheon, Koriya ta Kudu.[3]

Daga baya Msuya ta zama mai ba da shawara ga Mataimakin Shugaban Bankin Duniya na yankin Gabashin Asiya da Pasifik, wanda ke Washington, DC.[5][6]

Aiki a UNEP[gyara sashe | gyara masomin]

Daga shekarun 2018 zuwa 2021, Msuya ta yi aiki a matsayin Mataimakiyar Babban Darakta na Hukumar Kula da Muhalli ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNEP) a matakin Mataimakiyar Sakatare-Janar. Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya António Guterres ne ya naɗa ta a wannan matsayi a ranar 21 ga watan Mayu 2018, na tsawon shekaru 5.[5][7] Ta maye gurbin Ibrahim Thiaw na Mauritania, wanda ya cika wa'adinsa. [5]

Bayan murabus din Erik Solheim a watan Nuwambar 2018, an naɗa Msuya a matsayin Babbar Daraktar na UNEP.[8]

Rayuwa ta sirri[gyara sashe | gyara masomin]

Msuya tana da aure kuma tana da yara biyu.[5]

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Irene Tarimo – Tanzanian scientist, biologist and educator
  • Mary Mgonja – Tanzanian agricultural scientist

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Joyce Msuya of United Republic of Tanzania Appointed Assistant Secretary-General for Humanitarian Affairs, Deputy Emergency Relief Coordinator United Nations, press release of 14 December 2021.
  2. Joyce Msuya of United Republic of Tanzania Appointed Assistant Secretary-General for Humanitarian Affairs, Deputy Emergency Relief Coordinator United Nations, press release of 14 December 2021.
  3. 3.0 3.1 Yi Whan-woo (22 April 2014). "WB names chief for Korea office". The Korea Times. Seoul. Retrieved 22 May 2018.
  4. 4.0 4.1 George Mason University Korea (2016). "George Mason University Korea: Joyce Msuya, Member of the President's Advisory Board". Seoul: Masonkorea.gmu.edu. Archived from the original on 23 May 2018. Retrieved 22 May 2018.
  5. 5.0 5.1 5.2 5.3 Kelley, Kevin (22 May 2018). "Tanzanian lands senior UNEP post". The EastAfrican. Nairobi. Retrieved 22 May 2018.
  6. Namkwahe, John (22 May 2018). "Tanzanian lands top UN job". The Citizen (Tanzania). Dar es Salaam. Retrieved 22 May 2018.
  7. Azania Post Reporter (22 May 2018). "Tanzanian economist appointed to head UNEP". Dar es Salaam: Azaniapost.com. Archived from the original on 23 May 2018. Retrieved 22 May 2018.
  8. "Note to Correspondents on the resignation of Erik Solheim". United Nations Secretary-General. 20 November 2018. Retrieved 23 November 2018.