Zaynab Alkali

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Zaynab Alkali
Rayuwa
Haihuwa Jihar Borno, 1950 (73/74 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Hausawa
Harshen uwa Hausa
Karatu
Makaranta Jami'ar Bayero Bachelor of Arts (en) Fassara
Harsuna Turanci
Hausa
Larabci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a marubuci
Muhimman ayyuka The still born (en) Fassara
Imani
Addini Musulunci

Zaynab Alƙali (An haife ta a shekara ta 1950) ta kasance farfesa ce a harshen Turanci. Kuma ta fito ne daga gidan Turah-Mazila dake jihar Borno da jihar Adamawa.[1]

Kuruciya da Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Zainab Alkali ne a garin Tura-Mazila a jah

har Borno dake Arewacin kasar Najeriya a shekarar ta 195 Ta fara karatun ta na sakaadire a Queen Elizabet h,da kjiharar Illor. Sannan ta tafi zuwa Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, inda ta samu digirin ta na farko dana biyu. Daga baya ta koma Jami'ar Bayero dake jihar Kano shekarar a 1973 inda ta karanta turanci har ta kai ga ta samu digiri na uku wato matakin Dakta.[2]

Zainab Alkali ta shahara a rubuce-rubucen takaitattun kagaggun labarai, littafinta na farko data wallafa ya shahara, shi ne littafinta 'The Stillborn' a shekara ta 1984, sannan sai littafinta na biyu 'Virtuous woman' wadda Longman suka wallafa a shekara ta 1987, Zainab Alkali dai ta kasance marubuciya kuma ta wallafa littafai da dama, kuma littattafanta sun kasance an fassara su zuwa yaruka daban-daban kamar Jamusanci, larabci, Faransanci, Safaniyanci da dai sauran su. Tana daga cikin mata marubuta na farko a Arewacin Najeriya.

Rayuwarta[gyara sashe | gyara masomin]

Zainab ta auri tsohon shugaban jami'ar Maiduguri Mohammed Nur Alkali kuma suna da 'ya'ya shida tare.[3]

Ayyukan ta[gyara sashe | gyara masomin]

Littattafan ta[gyara sashe | gyara masomin]

Wanda ta gyara[gyara sashe | gyara masomin]

  • Zaynab Alkali, Al Imfeld (eds), Vultures in the Air: Voices from Northern Nigeria, Ibadan-Kaduna-Lagos: Spectrum Books, 1995, ISBN 978-978-2462-60-2

Girmamawa[gyara sashe | gyara masomin]

Nassi[gyara sashe | gyara masomin]

  • Kabir, Hajara Muhammad,. Mai talfawa matan arewicin. [Nijeriya]. ISBN 978-978-906-469-4. OCLC 890820657.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Kabir, Hajara Muhammad ([2010-]). Northern women development. [Nigeria]. ISBN 978-978-906-469-4. OCLC 890820657.
  2. Margaret Busby, Daughters of Africa, London: Cape, 1992, p. 782.
  3. Galleria, Nigeria. "Nigeria Personality Profile". Nigeria Galleria. Galleria Media Limited. Retrieved 11 March 2019.