Rikicin Zariya na 2015

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentRikicin Zariya na 2015
Map
 11°04′N 7°42′E / 11.07°N 7.7°E / 11.07; 7.7
Iri Kisan Kiyashi
Wuri Zariya

Yanar gizo islamicmovement.org

Rikicin Zariya na cikin shekarar 2015 rikici ne da ya faru tsakanin Sosojin Najeriya da yan kungiyar Harkar Musulunci a Najeriya (yan Shi'a mabiya Ibrahim Zakzaky) a birnin Zariya na Jihar Kaduna a Tataraiyar Najeriya. Anyi rikicin ne ranar 12 ga Disambar shekarar 2015.[1][2][3][4] Akalla fararen hula 348 ne suka rasa rayukan su, sannan kuma an binne wasu gawawaki 347 a rami ɗaya kuma a sirrance.[5]

Zaria a yau

Rundunar sojin Najeriya ta ce tabude wuta ne domin mayar da martani sakamakon ƙoƙarin da almajiran na Zazzaky sukayi na farmakar shugaban rundunar sosojin Najeriya Tukur Yusuf Buratai. Sai dai su yan shi'ar da wasu ƙungiyoyin kare Haƙƙin dan'adam sun musanta wannan bayanin na sosjoji, inda sukace rundunar sojin Najeriya ta afka masu ne batare da hakkin suba.[1][6][7][8].

Faruwar rikicin[gyara sashe | gyara masomin]

Ranar 12 ga Disamba shekarar 2015 ne a Zariya sojojin Najeriya suka koka kan cewar Yan Shi'a sun farmake su. Rikicin da yayi sanadiyyar mutuwar mutane 348 yayin da wasu da dama kuma suka sami raunuka.[4] Shima jagoran na ƙungiyar ta Harkar Musulunci a Najeriya Ibrahim Zakzaky ya samu raunika sakamakon harbi da harsahi da akayi masa tare kima da mai dakin sa da wasu daruruwan mabiyan nasho.[9]

An kone wasu da rayukan su, inji ƙungiyar kare Haƙƙin dan'adam ta kasar da ƙasa wato Amnesty International.[10]

Itama ƙungiyar kare Haƙƙin dan'adam ta Human Right Wach ta ce Gwamnatin Najeriya ta binne gawarwaki ba tare da sanin ahalin su ba.[11][12]

Yadda al'amarin ya shafi duniya[gyara sashe | gyara masomin]

Anyi zanga zangar lumana domin yin tir da lamarin a sassan wasu birane na kasar Indiya, wadanda suka hada da Mumbai, Chennai, da Hyderabad.[13][14][15] Haka nan ma anyi a Tehran da Mashhad na Iran.[16]

Bincike[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin Janairu na shekarar 2016, Gwamnatin Jihar Kaduna ta kafa kwamitin binciken musabbabin faruwar lamarin bisa ga jagorancin Maishari'a Mohammed Garba.[17][18]

Gano gaskiya[gyara sashe | gyara masomin]

Ranar 1 ga Ogas shekarar 2016, kwamitin ya samu bayanin cewar sojoji sun harbe mutum 328 yan Shi'a.[19].

Sake Karanta[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 "Nigerian Shiites Say Soldiers Have Killed Hundreds ",VOA NEWS, 14 December 2015.
  2. "Military, Shiite Muslims clash in northern Nigeria",Yahoo News, 14 December 2015.
  3. "Nigerian military attacks Shia group over blocked road, killing some",CNN News, 15 December 2015.
  4. 4.0 4.1 "Nigerian Shiites Say Soldiers Have Killed Hundreds",abcnews, 15 December 2015.
  5. Report of the Judicial Commission of Inquiry into the Clashes between the IMN and th NA in Zaria Archived 2021-03-05 at the Wayback Machine, July 2016.
  6. "Zaria Violent Clash: Army, Shiite sect trade blames",Vanguard Newspaper, 12 December 2015.
  7. "Zaria Massacre: Army had "predetermined mandate" to attack Shi'ites - Group - Premium Times Nigeria". Premium Times Nigeria (in Turanci). Retrieved 21 December 2015.
  8. LeVan, A. Carl; Ukata, Patrick (2018). The Oxford Handbook of Nigerian Politics (in Turanci). Oxford University Press. ISBN 9780198804307. Retrieved 24 July 2019.
  9. John, Maszka (27 October 2017). Al-shabaab And Boko Haram: Guerrilla Insurgency Or Strategic Terrorism? (in Turanci). World Scientific. ISBN 9781786344007.
  10. "NIGERIA: MILITARY COVER-UP OF MASS SLAUGHTER AT ZARIA EXPOSED". Retrieved 25 July 2019.
  11. "Mass graves for '300 Shia Nigerians' in Zaria". 23 December 2015. Archived from the original on 23 July 2019. Retrieved 25 July 2019.
  12. Jones, Sam (21 April 2016). "Nigerian army killed 350 and secretly buried the bodies, Amnesty says". The Guardian. Retrieved 8 August 2019.
  13. Ashish Tripathi (20 December 2015). "Shias in Lucknow want Indian govt to intervene in Nigerian crisis". The Times of India City. Retrieved 24 December 2015.
  14. K. A. Dodhiya (December 18, 2015). "Shias protest against killing in Nigeria". The Asian Age. Archived from the original on December 25, 2015. Retrieved December 24, 2015.
  15. Ashish Tripathi (21 December 2015). "Protest against the killings of Shia Muslims in Nigeria". The Siasat Daily, Hyderabad, India. Retrieved 24 December 2015.
  16. "Iranians protest against killing of Shias in Nigeria". Real Iran. 17 December 2015. Archived from the original on 30 June 2016. Retrieved 18 June 2016.
  17. "Justice Garba heads inquiry over Army-Shiite killings". TheNEWS. January 16, 2016. Retrieved 20 January 2016.
  18. Staff reporter (17 January 2016). "Shiíte Killings: Justice Mohammed Lawal Garba, other icons to lead inquiry". The Heraldng. Archived from the original on 27 January 2016. Retrieved 20 January 2016.
  19. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2016-09-20. Retrieved 2020-01-12.