Viola Onwuliri

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Viola Onwuliri
Ministan harkan kasan waje

2013 - 2014
Olugbenga Ashiru - Aminu Bashir Wali
Minister of State for Foreign Affairs of Nigeria (en) Fassara

2011 - 2015 - Khadija Bukar Ibrahim
Rayuwa
Haihuwa Mbaise (en) Fassara, 18 ga Yuni, 1955 (68 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƴan uwa
Abokiyar zama Celestine Onwuliri
Karatu
Makaranta Jami'ar Jos
Jami'ar Najeriya, Nsukka
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da biochemist (en) Fassara

Viola Adaku Onwuliri (An haifeta ranar 18 ga watan Yuni, 1956) lakcara ce, a jami'a a fannin koyar da darasin; ilmin kimiyyar nazari akan magungunan abubuwa masu rai-(Biochemistry), kuma ta kasance ƴar siyasa wadda ta taɓa zama ministan harkokin wajen Najeriya.

Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Viola Onwuliri ita ce ƴar fari, ta farko ga gidan Sarki Eze Cletus da Ugoeze Dorathy Oparaoji na Amuzi, Ahiazu Mbaise LGA, Jihar Imo.[1] Ta fito daga Ahiazu Mbaise a jihar Imo, Najeriya kuma an haife ta a birnin Legas a shekarar 1956. Ta halarci Makarantar Sakandaren Ƴan mata ta Owerri kafin Jami’ar Najeriya, Nsukka inda ta samu digiri na biyu da sakamakon/matakin (2nd Class Upper 2:1) a fannin Biochemistry.[1] Ta kuma halarci Jami'ar Jos inda ta sami digiri na PGCE, MSc a fannin Applied Organic Chemistry da PhD a Molecular Biochemistry. Sannan ta tafi kwasa-kwasan satifiket a Jami’ar Howard da Harvard School of Public Health da ke Amurka.[2]

Hillary Clinton ta samu tarba daga ministocin harkokin waje Olugbenga Ashiru da Viola Onwuli a shekarar 2012

Viola ta komo Najeriya inda ta samu aiki a shekarar 1981; a 2004 ta zama Farfesa a fannin Biochemistry 2004 a Jami'ar Jos.[ana buƙatar hujja] Ita da Mijinta, Celestine Onwuliri, sun haifi ƴaƴa biyar.

Memba a IAS[gyara sashe | gyara masomin]

A shekara ta 2004 Onwuliri ta zama ƴar Najeriya ta farko, kuma mace ta farko a nahiyar Afirka da aka zaɓe ta a matsayin memba a Geneva International AIDS Society (IAS) kuma ta zama wakiliyar yankin Afirka daga shekara ta 2004 zuwa 2008, har wayau an sake zaɓen ta a 2008 na tsawon shekaru huɗu.[3][4][5]

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Viola Onwuliri

A shekarar 2011 ta kasance mai neman zama mataimakiyar gwamnan jihar Imo kuma ta yi takara tare da Gwamna Ikedi Ohakim, [6] bayan sun sha kaye a zaɓen gwamnan jam’iyyar mai adawa Rochas Okorocha ya yi mata tayin muƙamin kwamishina a majalisar ministoci amma ta ki hakan ya bayar da mamaki. [7]

Daga baya ta zama ministar tarayya tare da jam’iyyarta kuma ta bayyana hakan ne a ranar 17 ga watan Oktoban 2013 ta jagoranci tawagar Najeriya wajen lashe kujerar majalisar ɗinkin duniya a zaɓen da aka gudanar shekaru biyu kacal bayan ficewa daga majalisar; ba a yi tsammanin cimma hakan ba sai nan da shekaru kusan 10. [8] [9] [10] [11]

Viola Onwuliri cikin wasu mutane

Har ila yau, ta kasance cikin hasashe a lokacin da ta yi kira ga shugaban Libya, Moammar Gadhafi, da ya yi murabus, tana mai cewa majalisar ƴan tawayen Libya ta fi wakilcin al'ummar Libya. [12] A wannan watan da ministar harkokin waje ta ziyarci wurin da aka kai harin bam a Ginin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Abuja wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 20. An jiyo ta tana cewa: “Wannan ba hari ne ga Najeriya ba, illa ga al’ummar duniya. An kai hari a duniya."[13]

Mutuwar mijinta a haɗarin Jirgi[gyara sashe | gyara masomin]

Bala'i ya afku a hatsarin jirgin Dana Air Flight 992 a watan Yunin 2012 wanda ya halaka mijinta Celestine Onwuliri da wasu mutane fiye da 150. Mijinta ya taɓa zama mataimakin shugaban jami'ar fasaha ta tarayya Owerri (FUTO). [14] [15] [16]

Ayyuka[gyara sashe | gyara masomin]

A matsayinta na matar mataimakin shugaban FUTO kuma shugabar ƙungiyar mata ta FUTO (FUTOWA) (2006-2011), [17] [18] ta taka muhimmiyar rawa wajen samar da ayyukan yi, ci gaban FUTO ta hanyar ƙungiyar, FUTOWA ciki har da samar da wuraren kula da yara ga ma'aikata da ɗalibai, kafa cibiyar bunƙasa yara da kuma ɗaukaka matsayin mata a FUTO. [7]

Viola Onwuliri

Ta haifar da ce-ce-ku-ce a karshen shekarar 2013 a matsayinta na Ministar Harkokin Waje a lokacin da ta buƙaci Gwamnan Imo a lokacin ya ba da lissafin kuɗaɗen da aka kashe daga Gwamnatin Tarayya da ya karɓa a madadin Jihar Imo, ciki har da (kuɗin); Sure-P Fund, magance zaizayar ƙasa., Kuɗaɗen Ambaliyar Ruwa, Kason Kudi na ƙananan hukumomi, Kason NDDC da sauran Kuɗaɗe [7] A matsayinta na Ministar Harkokin Waje ta yi ƙoƙari wajen sake kullawa da kyautata alaƙa da ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje, a matsayin mataki na farko na samar da yanayin da zai jawo hankalin ƴan Nijeriya mazauna ƙasashen waje a cikin harkar, Cimma ajandar/burin shugaban ƙasa da kuma jawo hankalin ƙaruwar zuba hannun jari kai tsaye na ƙasashen waje da kuma kuɗaɗen da ake turawa kai tsaye zuwa kasashen waje wanda ya kai dala biliyan 8 da dala biliyan 21 a lokacin mulkinta, [19] [20] tana aiki don inganta gami da mutuntawa da kuma kyautata mu'amalar ƴan Najeriya a cikin ƙasashen waje; Kuma ta zama ministar Najeriya ta farko da ta karɓi baƙuncin a hukumance a jami'ar Black University, Jami'ar Howard . [21] A matsayinta na Ministar Harkokin Wajen Najeriya daga 11 ga Yuli 2011-22 Oktoba 2014, wadda ta haɗa da zama minista-1-1 sannan ta zama minista mai kula da harkokin ƙasashen waje tsakanin 2013 zuwa 2014 kafin daga bisani ta koma ma'aikatar ilimi a matsayinta Jiha-1 Minista. [22]

Jagoranci[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin shekarar 2013, ta lashe shugabancin GlobalPOWER Women Network Africa. [23] Daga baya a shekarar da ta gabata, ta sami lambar yabo ta Tarayyar Turai, a Matsayin Jagorancin Platinum a Siyasa a ranar 28 ga Nuwamba 2013 a Stockholm, Sweden. [24]

Onwuliri ita ce shugabar ƙungiyar mata ta Afirka ta SWAAN kuma ta yi aiki a matsayin Babbar mai bincike da Daraktan Ayyuka tare da haɗin gwiwar Gidauniyar Bill da Melinda Gates . [25] [26] [27] Shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya mayar da Onwuliri daga ma’aikatar harkokin waje ya zama ƙaramin ministan ilimi a watan Oktoban 2014 lokacin da Ezenwo Nyesom Wike ya yi murabus. [28] [22]

A cikin 2015, gwamnatin Najeriya ta naɗa ta matsayin Pro-Chancellor na Jami'ar Maritime ta Najeriya (NMU) [29] [30] kuma a matsayin shugaban majalisa. [29] [31] [32]

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 "National Network Newspaper". National Network Newspaper (in Turanci). Retrieved 2020-05-24.
  2. Viola Onwuliri CV Archived 2015-11-23 at the Wayback Machine, Nigerian Embassy to Japan, Retrieved 10 February 2016
  3. , IAS Governing members Archived 2021-08-06 at the Wayback Machine, International AIDS Society, Retrieved 9 August 2018
  4. , IAS, IAS, Retrieved 9 August 2018
  5. Biography[permanent dead link], ECUDOMEF, Retrieved 9 August 2018
  6. Viola Adaku Onwuliri Archived 2018-07-08 at the Wayback Machine, Notable Nigerians, OnlineNigeria.com, Retrieved 10 February 2016
  7. 7.0 7.1 7.2 The Viola Onwuliri fear factor, 28 February 2014, Retrieved 8 August 2017
  8. , Nigeria Wins UN Security Council Seat, 18 Oct 2013, Retrieved 8 August 2017
  9. UN Security Council Needs NIgerias experience- Onwuliri Archived 2017-08-10 at the Wayback Machine, 2 December 2013, Retrieved 8 August 2017
  10. , UN Security Council- Onwuliri on the wheels of destiny, Independent Newspaper, 3 November 2013, Retrieved 8 August 2017
  11. , Nigeria wins United Nations Security Council Seat Archived 2017-08-10 at the Wayback Machine, Newsexpressngr, 17 October 2013, Retrieved 8 August 2017
  12. Nigeria Recognizes Libya Rebels, 22 August 2011,Voice of America, Retrieved 10 February 2016
  13. BBC (26 August 2011). "Abuja attack: Car bomb hits Nigeria UN building". BBC News. Retrieved 10 February 2016.
  14. [1] Archived 2017-08-10 at the Wayback Machine, Prof Onwuliri Condolence register, Retrieved 9 August 2018
  15. Knights Mourn leader Killed in plane crash, 9 June 2012, Dr.Ejaife, Retrieved 8 August 2017
  16. I Still Miss My Late Husband, Says Foreign Affairs Minister, Prof Viola Onwuliri, IMOTrumpet, Retrieved 10 February 2016
  17. , Viola Onwuliri raises NGN10million for FUTOWA projects 5 December 2009 Retrieved 14 August 2017
  18. , Viola Adaku Onwuliri Archived 2018-07-08 at the Wayback Machine, Online Nigeria,Retrieved 9 August 2017
  19. Nigeria attracts $8bn in Foreign Direct Investment – FGs, 9 August 2014 Retrieved 9 August 2017
  20. Foreign Direct Remittances[permanent dead link], 21 December 2016 Retrieved 9 August 2017
  21. Minister in the Diaspora, 16 November 2011 Retrieved 9 August 2017
  22. 22.0 22.1 Cabinet reshuffle: Onwuliri now Minister of Education (State), 22 October 2014, Retrieved 28 February 2016
  23. , Nigeria to head GlobalPower Women Network, 31 May 2013, Retrieved 8 August 2017
  24. , Hon Viola Onwuliri EU Award Archived 2018-07-08 at the Wayback Machine, 28 November 2013, Retrieved 8 August 2017
  25. Havard APIN Retrieved 9 August 2017
  26. APIN Retrieved 8 August 2017
  27. APIN, Retrieved 8 August 2017
  28. Viola Onwuliri, most performing minister, moved to fill Education 29 November 2014, Uncova Retrieved 14 August 2017
  29. 29.0 29.1 , Maritime University starts , 12 June 2015, Retrieved 8 August 2017
  30. , Nigerian Maritime University, 5 May 2017, Retrieved 8 August 2017
  31. , Amaechi and the Maritime University, 31 January 2016, Retrieved 9 August 2017
  32. , Delta Canvasses support for Maritime University, 10 June 2015, Retrieved 9 August 2017

Wikimedia Commons on Viola Onwuliri