Abduljabbar Nasuru Kabara

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Mukala mai kyau
Abduljabbar
Darul Kadiriyya, gidan da Abduljabbar yayi karatu a gaban mahaifin sa.
Sunan yanka Abduljabbar Nasuru Kabara
Haihuwa 07, Fabarairun 1970
Kano
Gurin zama Gwale Kano, Nigeria
Kasar asali Najeriya
Makaranta Ma'ahad
Uwar gida(s) 1
Yara Ba'asani ba
Dangi
  • Nasuru Kabara (Mahaifi)
  • Qaribullahi Nasuru Kabara (Dan uwa)
Yanar gizo ashabulkhafireporters.wordpress.com

Abduljabbar Nasuru Kabara (7 Fabarairu, 1970) An haife shi ne a ranar 7 ga watan Fabrairun, shekarar 1970, Malamin addinin Musulunci ne na Qadiriyya, wanda aka haife shi a jihar Kano, ya kasan ce ɗa ne ga Nasuru Kabara, tsohon shugaban Qadiriyya na Afirka, Abduljabbar malamin Qadiriyya ne wanda ake zargi da tozarci ga annabi muhammad (S.A.W).

Farko rayuwa

An haifi Abduljabbar ne a garin Kabara da ke cikin birnin jihar Kano, a Nigeria, ga dangin fitaccen shugaban Darikar Qadiriyyar Afirka Sheikh Nasuru Kabara, sunan mahaifiyarsa Hajiya Hafsah Adussamad, Shi ɗan uwa ne ga shugaban ɗarikar Ƙadiriyya na Afirka na yanzu, wanda aka fi sani da Qaribullahi Nasuru Kabara, ɗan uwansa ne yake jagorantar ɗarikar Ƙadiriyyan a Najeriya tun bayan rasuwar mahaifinsu, Sheikh Nasir Kabara, a shekarar 1996.[1][2]

Ilimi

Ya halarci Makarantar Ma'ahad kamar kowa daga dangin Kabara, Ya ci gaba da ɗabbaga karatun sa a makarantar Aliya da kuma ATC Gwale, daga baya ya koma Iraki don ci gaba da karatu, amma a cewar Abduljabbar ya ce ya sami mafi yawan karatunsa ne daga mahaifinsa kusan kimanin shekaru 25 na rayuwarsa.[3]

Aƙidar shi

Abduljabbar ta hanyar rayuwarsa sananne ne a matsayin mai bin darikar Kadiriyya kuma masani, yana bin sawun mahaifinsa, daga baya a kusan shekarar 2020 zuwa 2021, Ya bayyana aƙidar shi a matsayinsa mai harda da kaso mafi ya na hujjar Shi'a, yayin wata hira da yayi da BBC Hausa, yana cewa

Error: No text given for quotation (or equals sign used in the actual argument to an unnamed parameter)

— "bayan dogon binciken da nayi, na fahimci cewa Shi'a ma sunfi hujjoji fiye da Ahlussunna, wannan yasa nake ganin ba wani barazana da za'a ringa yimin akan ta " Ya ce" Ba zan damu ba idan kuka kira ni ɗan Shi'a ba, amma zan damu idan kuka kira ni dan Sunna."[4]

Rayuwar sa

Ɗa ne ga Sheikh Nasiru Kabara da Hajiya Hafsah Adussamad, Yana da aure da yara. Ya fi son Tuwon dawa tare da Miyar kuka da Naman rago, Yana son yawon buɗe ido zuwa Jihohi kamar Saudi Arabia, Iraq, Russia, Syria da United Arab Emirates .[5]

Mukabala

Gamayyar malaman addinin Musulunci a jihar Kano sun zargi Abduljabbar da yima Annabi Muhammad ƙazafi tare da cin zarafin Annabi da wasu daga cikin sahabbai da matayen Annabi. Malaman sun buƙaci gwamnatin jihar Kano da ta shirya masu zaman muƙabala a tsakanin su domin tantance da'awar makamin. A yayin zaman muƙabalar malamin ya gaza kare da'awar sa a gaban malamai lamarin da yasa gwamnatin jihar Kano kafa kwamitin bincike kan ainahin da'awar malamin.[6]

Suka

Ana kallan Abduljabbar a matsayin malami mai rigima na bangaran addinin Musulunci a jihar Kano, Manyan Malaman addinin Musulunci na Najeriya sun zargi Abduljabbar da yin Sabo da tozarci ga Annabi Muhammad da kuma Sahabban sa, Malaman sun yi jayayya da ƙin yarda da fatawar sa, malaman daga kungiyar Izala a Najeriya, Salafawa da kuma sauran malaman ƴan Ɗariku sun masa raddi, musamman ma ɗan uwan sa mai suna Qaribullahi Nasuru Kabara, ya barran ta daga dukkan fatwar sa, kuma ya ce fatawar sa bata da alaƙa da Ƙadiriya. A sakamakon sabo da dama da kuma hargitsin da'a ke tsoron aukuwar sa yasa Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Abdullahi Umar Ganduje ya sa aka rufe Masallacin sa tare da dakatar da Abduljabbar daga koyarwa da yin Da'awah a duk faɗin jihar ta Kano.[7][8][9] Abduljabbar yayin wata hira da BBC Hausa ya ce abin da gwamnatin jihar Kano ta yi masa na hana shi da'awa a jihar Kano rashin adalci ne.[10][11] gwamnatin jihar Kano kuma ta musanta rusa makarantar Abduljabbar a cikin jihar bayan jita jitar da suka ji a jihar.[12][13]

Hukuncin kisa

Kotun Shari'ar Muslunci mai zaman kanta a jihar Kano ta samu Abduljabbar da laifin Zagin Annabi Muhammad da cin zarafin wasu daga cikin Sahabbai da matayen Annabi da manyan malaman addinin Musulunci, inda Kotun ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya.[14] Tun da farko dai malamin ya sha ƙaryata zargin da ake masa inda ko da a lokacin da aka yanke masa hukuncin yake ta nanata cewar shiga ƙazafi ne aka yi masa.[15]

Haɗin waje

Duba kuma

Manazarta

  1. "The man Sheikh Abduljabbar Kabara – who's he?". Daily Trust (in Turanci). Retrieved 2021-02-26.
  2. "Ku San Malamanku tare da Sheikh Abduljabbar Kabara". BBC News Hausa. 2020-11-06. Retrieved 2021-02-26.
  3. https://dailytrust.com/the-man-sheikh-abduljabbar-kabara-whos-he
  4. "Ku San Malamanku tare da Sheikh Abduljabbar Kabara". BBC Hausa. 6 November 2020. Retrieved 2 February 2022.
  5. "Ku San Malamanku tare da Sheikh Abduljabbar Kabara". BBC News Hausa. 2020-11-06. Retrieved 2021-02-26.
  6. https://www.radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/2022/03/30/ana-zargin-gwamnatin-kano-na-son-yin-katsalandan-a-shariar-shaikh-abduljabbar/
  7. https://dailytrust.com/kano-debars-sheikh-abduljabar-for-incitement-shuts-seminaries
  8. https://www.rfi.fr/ha/najeriya/20210205-abdul-jabbar-makaryaci-ne-ganduje
  9. https://freedomradionig.com/kano-abubuwa-bakwai-da-ganduje-ya-fada-akan-abduljabbar-nasiru-kabara/
  10. https://www.dw.com/ha/kano-martani-kan-hana-wani-malami-waazi/a-56458920
  11. https://www.bbc.com/hausa/labarai-55937439
  12. https://www.voahausa.com/a/gwamnatin-kano-ta-musunta-rusa-makarantar-sheikh-abduljabbar-nasiru-kabara/5768039.html
  13. "Gwamnatin Kano Ta Musanta Rusa Makarantar Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara". VOA. Retrieved 2021-02-26.
  14. https://hausa.legit.ng/news/1509715-kai-tsaye-daga-kotu-yadda-shariar-abduljabbar-kabara-ke-gudana/
  15. https://hausa.leadership.ng/abduljabbar-ne-ya-kirkiri-kalaman-batanci-ga-annabi-muhammad-saw-kotu/