Abdulsalami Abubakar
![]() | |||||
---|---|---|---|---|---|
![]() | |||||
8 ga Yuni, 1998 - 29 Mayu 1999 ← Sani Abacha - Olusegun Obasanjo →
21 Disamba 1997 - 9 ga Yuni, 1998 | |||||
Rayuwa | |||||
Haihuwa | Minna, 13 ga Yuni, 1942 (80 shekaru) | ||||
ƙasa |
Colony and Protectorate of Nigeria (en) ![]() Taraiyar Najeriya First Nigerian Republic (en) ![]() Jamhuriyar Najeriya ta biyu Najeriya | ||||
Harshen uwa |
Gbagyi (en) ![]() | ||||
Ƴan uwa | |||||
Abokiyar zama | Fati Lami Abubakar | ||||
Karatu | |||||
Harsuna |
Gbagyi (en) ![]() Turanci Hausa Pidgin na Najeriya | ||||
Sana'a | |||||
Sana'a | ɗan siyasa da soja | ||||
Digiri | Janar | ||||
Imani | |||||
Addini | Musulunci | ||||
Jam'iyar siyasa | no value |
Abdulsalami Abubakar Tsohon janar din Soja ne kuma ɗan Siyasa a Najeriya da yayi mulki na dan lokaci sannan ya miqawa farar hula a tsakanin shekarata 1998 zuwa 1999.[1] An haife shi a shekara ta 1942 a birnin Minna, Jihar Neja dake arewacin Najeriya (a yau jihar Neja). Abdulsalami Abubakar yazama shugaban kasar Nijeriya bayan rasuwar Janar Sani Abacha, yayi mulki daga watan Yunin shekara ta 1998 zuwa watan Mayu 1999 (bayan Sani Abacha - kafin Olusegun Obasanjo).
A lokacin mulkinshi ne Najeriya ta fidda sabon kundin tsarin mulki wato 1979 constitution, wanda ta bada daman zabe tsakanin jam'iyyu daban daban. Abdulsalam ya mika madakon iko ga sabon zababben shugaba Olusegun Obasanjo a ranar 29 ga watan Mayu shekara ta 1999. Shine Chairman na yanzu na National Peace Committee.[2]
Kuruciya[gyara sashe | gyara masomin]
An haifi Abdulsalam daga dangin Hausawa a ranar 13 ga watan Yuni shekara ta 1942, mahaifinsa shine Abubakar Jibrin tare da mahaifiyarsa Fatikande Mohammed a Minna, Jihar Neja, Najeriya.
Abdulsalam ya halarci Minna Native Authority Primary school a tsakanin shekarar 1950 zuwa 1956. A tsakanin shekara ta 1957 zuwa 1962 yayi karatunsa na sakandare a Government College, Bida, jihar Neja.
Aikin Soja[gyara sashe | gyara masomin]
Sojin Sama[gyara sashe | gyara masomin]
Abdulsalam na cikin fitattun daliban sojan sama da suka fara a ranar 3 ga watan Octoba shekara ta 1963. A tsakanin shekara ta 1964 zuwa 1966, an dauke su zuwa garin Uetersen dake yammacin kasar Germany domin kara samun horo na musamman. A lokacin da suka dawo Najeriya a shekara ta 1966, an mayar dashi zuwa sojin kasa.
Rayuwarsa a matsayin sojan kasa[gyara sashe | gyara masomin]
Bayan ya cigaba a matsayin sojan kasa a 1966, Abubakar ya ziyarci Short service combatant two, inda ya fito a matsayin second lieutenant a watan October shekara ta 1967, a sahib yaki. A tsakanin shekara ta 1967 zuwa 1968 Abdulsalam Abubakar ya riqe matsayin General Staff Officer two, garrison officer sannan kuma commanding officer, sannan kuma 92 infantry batallion a tsakanin shekarar 1969 zuwa 1974. A tsakanin shekarar 1974 zuwa 1975 an bashi matsayin brigade manjo bataliyar yaki na 7. A shekarar 1975 yayi aiki a matsayin commanding officer, bataliyar yaki na 84. Har wayau, tsakanin shekara ta 1978 zuwa 1979 Abdulsalam ya riqe matsayin commanding officer na bataliyar yaki na 145 (NIBATT II), United Nations Interim force, dake kasar Lebanon.
Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]
- ↑ Abubakar, Abdulsalam (2015). Financial development, impact on output and its determinants: the case of the economic community of the West African states. Kulliyyah of Economics and Management Sciences, International Islamic University Malaysia.
- ↑ "Buhari, Abdulsalami's national peace committee meet". Punch Newspapers. Retrieved 29 May 2020.