Abdulsalami Abubakar

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abdulsalami Abubakar
shugaban ƙasar Najeriya

8 ga Yuni, 1998 - 29 Mayu 1999
Sani Abacha - Olusegun Obasanjo
Chief of the Defence Staff (en) Fassara

21 Disamba 1997 - 9 ga Yuni, 1998
Rayuwa
Haihuwa Minna, 13 ga Yuni, 1942 (81 shekaru)
ƙasa Colony and Protectorate of Nigeria (en) Fassara
Taraiyar Najeriya
Jamhuriyar Najeriya ta farko
Jamhuriyar Najeriya ta biyu
Najeriya
Harshen uwa Gbagyi
Ƴan uwa
Abokiyar zama Fati Lami Abubakar
Karatu
Harsuna Gbagyi
Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da soja
Digiri Janar
Imani
Addini Musulunci
Jam'iyar siyasa no value
Abdulsami Abubakar

Abdulsalami Abubakar Tsohon janar ɗin Soja ne kuma ɗan Siyasa a Najeriya da yayi mulki na ɗan lokaci sannan ya miƙawa farar hula a tsakanin shekara ta alif ɗari tara da casa'in da takwas 1998A.c) zuwa shekarar alif ɗari tara da casa'in da tara 1999.[1] An haife shi a shekara ta alif ɗari tara da arba'in da biyu 1942 a birnin Minna, Jihar Neja dake arewacin Najeriya (a yau jihar Neja). Abdulsalami Abubakar yazama shugaban ƙasar Najeriya bayan rasuwar Janar Sani Abacha, yayi mulki daga watan Yunin shekara ta alif ɗari tara da chasa'in da takwas 1998 zuwa watan Mayun shekarar alif ɗari tara da chasa'in da tara 1999 (bayan Sani Abacha - kafin Olusegun Obasanjo).

A lokacin mulkinshi ne Najeriya ta fidda sabon kundin tsarin mulki wato 1979 constitution, wanda ta bada daman zaɓe tsakanin jam'iyyu daban daban. Abdulsalam ya miƙa madakon iko ga sabon zaɓaɓɓen shugaba Olusegun Obasanjo a ranar 29 ga watan Mayu shekara ta alif ɗari tara da chasa'in da tara 1999. Shine Chairman na yanzu na National Peace Committee.[2]

Kuruciya[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Abdulsalam daga dangin Hausawa a ranar 13 ga watan Yuni shekara ta alif ɗari tara da arba'in da biyu 1942, mahaifinsa shine Abubakar Jibrin tare da mahaifiyarsa Fatikande Mohammed a Minna, Jihar Neja, Najeriya.

Abdulsalam ya halarci Minna Native Authority Primary school a tsakanin shekarar alif ɗari tara da hamsin 1950 zuwa shekarar alif ɗari tara da hamsin da shida 1956. A tsakanin shekara ta alif ɗari tara da hamsin da bakwai 1957 zuwa shekarar alif ɗari tara da sittin da biyu 1962 yayi karatunsa na sakandare a Government College, Bida, jihar Neja.

Aikin Soja[gyara sashe | gyara masomin]

Sojin Sama[gyara sashe | gyara masomin]

Abdulsalam na cikin fitattun ɗaliban sojan sama da suka fara a ranar 3 ga watan Octoba shekara ta alif ɗari tara da sittin da uku 1963. A tsakanin shekara ta alif ɗari tara da sittin da huɗu 1964 zuwa shekarar alif ɗari tara da sittin da shida 1966, an ɗauke su zuwa garin Uetersen dake yammacin ƙasar Germany domin ƙara samun horo na musamman. A lokacin da suka dawo Najeriya a shekara ta alif ɗari tara da sittin da shida 1966, an mayar dashi zuwa sojin ƙasa.

Rayuwarsa a matsayin sojan kasa[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan ya cigaba a matsayin sojan ƙasa a shekarar alif ɗari tara da sittin da shida 1966, Abubakar ya ziyarci Short service combatant two, inda ya fito a matsayin second lieutenant a watan October shekara ta alif ɗari tara da sittin da bakwai 1967, a sahib yaki. A tsakanin shekara ta alif ɗari tara da sittin da bakwai 1967 zuwa shekarar alif ɗari tara da sittin da takwas 1968 Abdulsalam Abubakar ya riƙe matsayin General Staff Officer two, Garrison officer sannan kuma Commanding officer, sannan kuma 92 infantry batallion a tsakanin shekarar alif ɗari tara da sittin da tara 1969 zuwa shekara ta alif ɗari tara da saba'in da huɗu 1974. A tsakanin shekarar alif ɗari tara da saba'in da huɗu 1974 zuwa shekarar alif ɗari tara da saba'in da biyar 1975 an bashi matsayin Brigade manjo bataliyar yaki na 7. A shekarar alif ɗari tara da saba'in da biyar 1975 yayi aiki a matsayin commanding officer, bataliyar yaƙi na 84. Har wayau, tsakanin shekara ta alif ɗari tara da saba'in da takwas 1978 zuwa shekarar alif ɗari tara da saba'in da tara 1979 Abdulsalam ya riƙe matsayin commanding officer na bataliyar yaƙi na 145 (NIBATT II), United Nations Interim force, dake ƙasar Lebanon.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Abubakar, Abdulsalam (2015). Financial development, impact on output and its determinants: the case of the economic community of the West African states. Kulliyyah of Economics and Management Sciences, International Islamic University Malaysia.
  2. "Buhari, Abdulsalami's national peace committee meet". Punch Newspapers. Retrieved 29 May 2020.